Babban Ma’aikacin Fadar Shugaban Kasa, Femi Gbajabiamila, ya bayyana sabon Karamin Ministan Harkokin Wajen Najeriya, Ambassador Sola Enikanolaiye, a matsayin mutum mai matukar amfani ga kasa.
Gbajabiamila ya bayyana hakan ne a wani bikin bankwana da aka shirya masa a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja bayan nadinsa a matsayin Karamin Ministan Harkokin Waje.
Ya ce gogewar Enikanolaiye a harkokin diflomasiyya, ilimi da hulda da kasashen duniya ta shirya shi sosai domin gudanar da sabon mukaminsa.
A cewarsa, lokacin da ya karbi aiki a matsayin Babban Ma’aikacin Fadar Shugaban Kasa, an gabatar masa da sunaye uku domin zabar Mataimaki na Musamman kan Harkokin Waje, kuma ya zabi Enikanolaiye duk da cewa bai san shi ba a lokacin.
Gbajabiamila ya yaba da kwazonsa, jajircewarsa da kuma kwarewarsa wajen gudanar da aiki, yana mai cewa babu shakka zai yi nasara a duk inda aka tura shi.
Ya kuma yabawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa daukaka Enikanolaiye zuwa mukamin minista, yana mai cewa Najeriya za ta amfana matuka daga iliminsa da gogewarsa.
A nasa jawabin, Enikanolaiye ya gode wa Shugaba Tinubu da ya ba shi damar yi wa kasa hidima, tun daga mukamin Mataimaki na Musamman kan Harkokin Waje har zuwa sabon mukamin minista.
Ya kuma gode wa Gbajabiamila bisa kyakkyawan yanayin aiki da ya samar wanda ya taimaka wajen bunkasa aiki da nasarori.
Sabon ministan ya bukaci ma’aikata su rungumi aiki tukuru, kyakkyawar mu’amala da juna da kuma mutunta bambance-bambancen addini da al’adu.
Ya bayyana cewa shi Musulmi ne yayin da matarsa Kirista ce, yana mai cewa bambance-bambancen addini bai kamata su zama sanadin rikici a cikin al’umma ba.
Ambasada Sola Enikanolaiye ya fito ne daga garin Igbagun a Jihar Kogi State. Ya kammala karatun Digiri na Farko a fannin Kimiyyar Siyasa daga Ahmadu Bello University a shekarar 1981 inda ya zama dalibi mafi hazaka a jami’ar a shekarar.
Ya shiga Ma’aikatar Harkokin Waje ta Najeriya a shekarar 1982, sannan ya yi aiki a ofisoshin jakadancin Najeriya da dama kafin ya zama Babban Sakataren Ma’aikatar Harkokin Waje a shekarar 2016. Ya yi ritaya daga aikin gwamnati a shekarar 2017 bayan shekaru 35 yana yi wa k9asa hidima.
