Daliban Jami’ar Adekunle Ajasin da ke Akungba-Akoko (AAUA) a Jihar Ondo na ci gaba da fuskantar rashin tabbas sakamakon yajin aikin da Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU) reshen jami’ar ta fara saboda rashin biyan albashin watannin Mayu da Yuni na shekarar 2026.
ASUU ta fara yajin aikin ne daga 10 ga Yuli, 2026, bayan taron majalisar kungiyar, inda ta bayyana cewa matakin ya kasance cikakke kuma ba zai ƙare ba har sai an biya dukkan albashin da ake bin malaman.
Sakamakon yajin aikin, an dakatar da laccoci, kula da ayyukan ɗalibai, tarurruka da sauran ayyukan ilimi, lamarin da ya jefa dubban ɗalibai cikin damuwa.
Rahotanni sun nuna cewa jarabawar zangon karatu na biyu da aka tsara farawa a 20 ga Yuli ta shiga rudani, musamman ga ɗaliban ajin ƙarshe da ke fatan kammala karatunsu cikin lokaci.
Kungiyar Daliban Jami’ar (AAUASU) ta bayyana cewa yajin aikin ya shafe sama da kwanaki 14, tare da haifar da cikas ga kalandar karatu da kuma jefa ɗalibai cikin damuwa ta fuskar ilimi, tunani da tattalin arziki.
Kungiyar ta kuma bai wa Gwamnatin Jihar Ondo wa’adin sa’o’i 72 domin ta kawo mafita ga rikicin, tana mai gargadin cewa idan ba a dauki mataki ba za ta bi hanyoyin da doka ta tanada wajen bayyana damuwarta.
Sai dai mahukuntan jami’ar sun bayyana cewa gwamnati ta riga ta fara daukar matakan warware matsalar.
A wata sanarwa da Mataimakin Magatakardar Jami’ar mai kula da hulɗa da jama’a, Sola Imoru, ya sanya wa hannu, jami’ar ta ce Gwamna Lucky Orimisan Aiyedatiwa, wanda shi ne Baƙon Jami’ar, ya amince da asusun tallafin gaggawa domin biyan wasu daga cikin basussukan da ake bin jami’ar.
Mahukuntan jami’ar sun ce an fara shirye-shiryen fitar da kuɗaɗen, tare da roƙon ɗalibai da su kwantar da hankalinsu yayin da ake kammala tsarin biyan kuɗin.
Jami’ar ta kuma buƙaci shugabannin ƙungiyar ɗalibai da su riƙa neman cikakken bayani daga mahukunta kafin fitar da sanarwa ga jama’a.
Rikicin ya sake bayyana irin tasirin da yawan yajin aikin jami’o’i ke yi ga tsarin ilimi a Najeriya, inda ɗalibai ke rasa lokacin karatu, jinkirin jarabawa da kammala karatu, yayin da malamai ke neman haƙƙoƙinsu na albashi.
Yayin da malamai ke jiran a biya su abin da suka cancanta, ɗalibai da iyayensu na ci gaba da fatan gwamnati da jami’a za su warware rikicin cikin gaggawa domin dawo da karatu yadda ya kamata.
