Jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) ta bukaci shugabannin Najeriya a dukkan matakai da su gudanar da mulki cikin gaskiya, kishin kasa da kuma biyayya ga manufofin dimokuradiyya yayin bikin Ranar Dimokuradiyya ta shekarar 2026.
A cikin wata sanarwa da Sakataren Yada Labarai na Kasa na jam’iyyar, Zakari Yau Nadabo, ya fitar, SDP ta bayyana cewa ranar 12 ga Yuni na da muhimmiyar matsayi a tarihin siyasar Najeriya domin tana wakiltar nasarar muradin al’umma, adalci da shugabanci nagari.
Jam’iyyar ta tunatar da cewa marigayi Chief Moshood Kashimawo Olawale Abiola ya tsaya takarar shugaban kasa karkashin SDP kuma ya lashe zaben ranar 12 ga Yunin 1993, wanda har yanzu ake kallonsa a matsayin mafi sahihanci da gaskiya a tarihin Najeriya.
SDP ta yabawa jaruman gwagwarmayar dimokuradiyya, kungiyoyin fararen hula, ‘yan jarida da sauran ‘yan Najeriya da suka sadaukar da kai wajen tabbatar da dawowar mulkin dimokuradiyya a kasar nan.
A cewar jam’iyyar, ranar 12 ga Yuni ba ranar tunawa kadai ba ce, har ila yau lokaci ne na yin nazari kan muhimmancin adalci, gaskiya, hadin kai, rikon amana da mutunta zabin jama’a.
Jam’iyyar ta jaddada cewa dorewar ruhin 12 ga Yuni na bukatar karfafa cibiyoyin dimokuradiyya, gudanar da sahihan zabuka, kare hakkin ‘yan kasa da kuma samar da shugabanci mai sauraron bukatun al’umma.
SDP ta sake tabbatar da kudirinta na ci gaba da kare darajojin dimokuradiyya, ci gaban kasa, adalci da walwalar ‘yan Najeriya baki daya.
Jam’iyyar ta kuma bukaci ‘yan kasa su ci gaba da shiga harkokin siyasa cikin lumana tare da rike shugabanni da alhakin ayyukansu domin tabbatar da ingantaccen shugabanci.
A karshe, SDP ta bayyana fatanta na ganin Najeriya mai cike da adalci, dama ga kowa da kuma kasa inda muryar kowanne dan kasa ke da muhimmanci.
