Mataimakin ɗan takarar gwamnan jihar Kaduna na jam’iyyar APC, Jerry Adams, ya yi kira ga al’ummar Kudancin Kaduna, mabiya addinin Kirista da sauran mazauna jihar da su ci gaba da goyon bayan gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu da Gwamna Uba Sani a zaɓen 2027.
Adams, wanda tsohon shugaban Hukumar Tattara Haraji ta Jihar Kaduna ne, KADIRS, kuma Gwamna Uba Sani ya zaɓe shi a matsayin abokin takararsa, ya ce Kudancin Kaduna zai fi samun ci gaba idan APC ta sake samun nasara a zaɓen shugaban ƙasa, na gwamna da sauran mukamai a 2027.
Adams ya bayyana hakan ne a yayin taron Choral Convention na 2026 karo na 31 da aka gudanar a Kaduna, mai taken “Let Your Light Shine”, inda wakilinsa, Samuel Atung, SAN, ya gabatar da saƙon.
Ya ce a ƙarƙashin gwamnatin Tinubu da Uba Sani, Kudancin Kaduna ya samu ayyukan more rayuwa da dama, tare da samun wakilci ta hanyar naɗa ‘ya’yan yankin a muƙamai daban-daban na gwamnatin tarayya da jiha.
Ya buƙaci al’ummar yankin da su rama irin wannan kulawa ta hanyar bai wa shugabannin da suka nuna ƙwazo da jajircewa wajen ci gaban jama’a goyon baya.
Adams ya kuma yaba da salon mulkin Gwamna Uba Sani, musamman yadda ya ce gwamnatin ta mai da hankali wajen rarraba ayyukan raya ƙasa a sassan jihar Kaduna.
Haka kuma, ya bayyana Sanata Sunday Marshall Katung a matsayin ɗan takara mai dacewa da wakiltar Kudancin Kaduna a zaɓen Sanata, yana mai yabawa da ayyukan da ya gabatar a Majalisar Dattawa da gudummawar da yake bayarwa ga al’ummar yankin.
Ya buƙaci jama’a da su daina kallon siyasa ta fuskar jam’iyya kawai, su fi mayar da hankali kan ayyukan shugabanni da irin gudummawar da suka bayar wajen inganta rayuwar al’umma.
Adams ya kuma yi kira ga Kiristoci da al’ummar Kudancin Kaduna da su kasance masu haɗin kai tare da taka muhimmiyar rawa a harkokin siyasa gabanin zaɓen 2027, yana mai cewa ya kamata su yi amfani da ƙuri’unsu wajen tabbatar da ci gaba da tallafa wa shugabannin da suka nuna kishin jama’a.
An shirya taron Choral Convention ne tare da haɗin gwiwar Non-denominational Christian Association of Nigeria (NCCN) da Christian Association of Nigeria (CAN) domin yabon Allah ta hanyar waƙoƙi da ibada.
