Jarumi kuma mai shirya fina-finai, Yomi Fabiyi, ya yi kira da a gudanar da cikakken bincike kan mutuwar jarumar Nollywood, Temitope Osoba, tare da yin gwajin gawarta (autopsy) kafin a gudanar da jana’izarta.
Fabiyi ya bayyana cewa Osoba da kanta ta kai rahoton wani lamari ga ‘yan sanda, inda ta nuna cewa akwai yiwuwar aikata laifi. Sai dai ya ce ta rasu bayan ‘yan sa’o’i, ba tare da ganin an gudanar da bincike mai zurfi kan lamarin ba.
Ya ce, “Tope Osoba da kanta ta kai rahoton lamarin ga ‘yan sanda kuma ta nuna cewa akwai bangaren laifi. Ta rasu bayan ‘yan sa’o’i, amma babu wanda ya nuna sha’awar gudanar da bincike.”
Jarumin ya kuma nuna damuwa kan shirin binne Osoba ba tare da an gudanar da autopsy ba, yana mai cewa ya kamata a bar hukumomi su bi matakan da doka ta tanada domin gano hakikanin abin da ya haddasa mutuwar.
Ya ce idan ana son tabbatar da adalci da kuma gano gaskiyar lamarin, bai kamata a yi gaggawar binne gawar ba kafin a kammala bincike.
Fabiyi ya tabbatar da cewa kungiyarsa za ta ci gaba da binciken lamarin ko da an gudanar da jana’izar kamar yadda aka tsara.
Ya ce, “Ko an yi jana’iza ko ba a yi ba, za mu ci gaba da bincikenmu har sai mun gano tushen lamarin. Doka za ta yi aikinta idan lokaci ya yi.”
Haka kuma, ya yi kira ga al’umma da kada motsin rai ko son zuciya su hana gudanar da bincike kan mutuwa ko zargin aikata laifi.
Mutuwar Osoba ta kasance abin mamaki a masana’antar Nollywood, bayan da abokin aikinta, Alesh Sanni, ya sanar da rasuwarta a shafinsa na Instagram, inda ya bayyana ta a matsayin ‘yar’uwarsa ta ƙwarai.
Mutuwar jarumar ta zo ne kimanin shekaru biyu bayan ta bayyana cewa tana fama da cutar kansar nono. Daga baya ta sanar da cewa ta warke, inda a watan Agustan 2025 ta bayyana komawarta harkar fim tare da mai da hankali wajen wayar da kan jama’a kan cutar kansar nono.
Bayan rasuwarta, iyalan Awonuga/Osoba sun gargadi jama’a da su guji yada rahotannin da ba a tabbatar da su ba ko kuma bayanan da ba su samu izini daga iyalan ba. Sun bukaci jama’a su dogara da bayanan da iyalan suka tabbatar.
An tsara binne Osoba a ranar Alhamis, 13 ga Agusta, 2026, a Iperu Remo, Jihar Ogun. Ana sa ran za a gudanar da addu’ar jana’izarta a Saint James Anglican Church, Iperu Remo, kafin a kai gawarta makabarta.
A gefe guda, angonta, Prophet Itunu Onadeko, ya yi wasu zarge-zarge kan abubuwan da suka faru a lokutan karshe na rayuwarta. Ya yi ikirarin cewa ta rasu a wani ofishin ‘yan sanda da ke Ikorodu, Lagos, duk da cewa ya ce bai san takamaiman ofishin ba.
Onadeko ya kuma musanta rade-radin cewa mutuwarta ta samo asali ne daga matsalolin cutar kansar nono da ta taba fama da ita, tare da yin watsi da wasu zarge-zarge da suka biyo bayan mutuwarta.
Sai dai wasu daga cikin iyalanta sun bayar da wani bayanin daban kan lokutan karshe na rayuwarta. Kawarta ta wajen uwa, Pejuola Ogunesan, ta ce Osoba ta taba yin maganar cewa tana ganin mutuwarta na gabatowa, sannan yanayinta ya kara tsananta kafin a kai ta asibiti.
Ya zuwa yanzu, ba a tabbatar da wadannan bayanai masu karo da juna ba ta hanyar bincike mai zaman kansa.
Kiran Fabiyi na yin autopsy da gudanar da cikakken bincike ya kara jawo hankalin jama’a kan bukatar gano gaskiyar abin da ya faru da jarumar kafin a rufe shafin lamarin.
