Gwamnan Jihar Kaduna, Uba Sani, ya amince da naɗin Alhaji Suleiman Sa’ad Abubakar a matsayin sabon Emir na Kagarko.
A wata sanarwa da Kwamishinan Ƙananan Hukumomi, Alhaji Sadiq Mamman Lagos, ya fitar a ranar Litinin, an bayyana cewa naɗin ya fara aiki nan take.
Sanarwar ta ce sabon Emir, wanda ya rike muƙamin San Turakin Kagarko, ya fito ne bayan tsauraran tsarin zaɓe da tantancewa da aka gudanar.
A cewar Kwamishinan, masu zaɓen sarauta na Majalisar Masarautar Kagarko ne suka yi tantancewa tare da duba ‘yan takara da dama kafin a zaɓi Suleiman Sa’ad Abubakar.
Sanarwar ta kuma tuna cewa an yi wannan naɗi ne bayan rasuwar tsohon Emir na biyu a daraja na Kagarko, Alhaji Sa’ad Abubakar, wanda ya rasu a ranar 8 ga Janairu, 2026, bayan ya shafe shekaru shida a kan karaga.
Gwamna Uba Sani ya taya sabon Emir murna, tare da yi masa fatan zaman lafiya da ci gaban masarauta.
Haka kuma an bayyana cewa za a sanar da ranar bikin nadin sarautar da miƙa sandar mulki (staff of office) a nan gaba.
Sanarwar ta ƙara da cewa gwamnati ta bukaci sabon Emir ya ci gaba da inganta zaman lafiya da haɗin kai a cikin al’umma.
