Kungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN) ta yi kakkausar suka kan harin da ‘yan bindiga suka kai wa wani taron coci a Eda Oniyo da ke karamar hukumar Ilejemeje a jihar Ekiti, inda aka kashe fasto tare da sace wasu masu ibada da dama.
Lamarin ya faru ne a daren Talata da misalin karfe 8:30 na dare yayin da masu ibada ke gudanar da shirin coci cikin lumana, kafin ‘yan bindigar suka kutsa cikin cocin Christ Apostolic Church, suka bude wuta, suka kashe faston nan take sannan suka yi awon gaba da wasu daga cikin masu ibadar zuwa cikin daji.
Wannan mummunan hari ya jefa al’ummar yankin cikin firgici, inda mazauna garin ke nuna tsananin damuwa kan karuwar matsalar tsaro a yankin.
A cikin wata sanarwa da shugaban CAN, Archbishop Daniel Okoh, ya fitar a ranar Laraba, ya bayyana harin a matsayin abu mai matukar tayar da hankali da tashin hankali.
“kungiyar tabaiyana cewa Mun yi Allah-wadai da wannan danyen aiki mafi muni. Mutane sun taru ne domin bautar Ubangiji cikin zaman lafiya, amma aka tarbe su da tashin hankali. Wannan ba hari kan coci kadai ba ne, hari ne kan rayuwa, imani da kuma mutuncin bil’adama baki daya.”
CAN ta mika ta’aziyya ga iyalan faston da aka kashe tare da nuna cikakken goyon baya ga sauran wadanda abin ya shafa da daukacin al’ummar Kirista a jihar Ekiti.
Kungiyar ta kuma bukaci hukumomin tsaro da gwamnati su gaggauta daukar mataki domin ceto wadanda aka sace cikin koshin lafiya.
“Muna addu’a tare da iyalan mamacin faston, muna kuma kira da a sako dukkan wadanda aka sace ba tare da bata lokaci ba.”
CAN ta danganta harin da yawaitar matsalar rashin tsaro a wasu sassan Najeriya, tana mai nuni da irin hare-haren da ake samu a wasu jihohi kamar Kogi, inda ake kai hare-hare kan al’umma da limamai.
Kungiyar ta gargadi cewa ci gaba da kai hare-hare kan wuraren ibada da yankunan karkara na kara jefa jama’a cikin tsoro da rashin kwanciyar hankali.
Ta jaddda cewa Kare rayuka da dukiyoyin al’umma babban nauyi ne da ya rataya a wuyan gwamnati. Dole ne hukumomin tsaro su dauki matakan gaggawa, masu karfi kuma a bayyane domin kamo masu hannu a wannan aika-aika tare da gurfanar da su a gaban kuliya.”
CAN ta kuma bukaci a kara yawan jami’an tsaro a yankunan karkara da wuraren da ke cikin hadari, tare da inganta tattara bayanan sirri domin hana sake aukuwar irin wannan hari a gaba.
