Majalisar Wakilai ta amince da bukatar Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta karbo bashin dala miliyan 516.33 daga Deutsche Bank domin fara aikin sashe na farko na babbar hanyar Sokoto zuwa Badagry, daya daga cikin manyan ayyukan raya kasa karkashin shirin Renewed Hope Agenda.
Amincewar ta zo ne bayan tattaunawa da nazarin bukatar shugaban kasa a zaman majalisar da Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, ya jagoranta.
A cikin wasikar da aka karanta a zauren majalisar, Tinubu ya bayyana aikin hanyar Sokoto-Badagry a matsayin babban aikin kasa mai matukar muhimmanci wanda zai hada yankin Arewa maso Yamma da yankin Kudu maso Yamma ta hanyar kusan kilomita 1,000 daga Illela a Sokoto zuwa Badagry a jihar Legas.
Ana sa ran hanyar za ta ratsa jihohin Sokoto, Kebbi, Niger, Kwara, Oyo, Ogun da Lagos, inda hakan zai bude manyan cibiyoyin noma, kasuwanci da masana’antu a fadin kasar.
Shugaban kasar ya ce aikin zai taimaka wajen bunkasa tattalin arziki sosai ta hanyar saukaka zirga-zirgar kayayyaki da mutane tsakanin Arewa da Kudu.
Tinubu ya kuma bayyana cewa an tsara hanyar ne ta yadda za a samar da damar shimfida layin dogo a gaba a tsakiyar hanyar, tare da hanyoyin samar da sauran muhimman kayayyakin more rayuwa.
Shugaban ya bayyana Cewa Deutsche Bank zai bayar da dala miliyan 516.33
Islamic Development Bank zai bayar da kariyar wani bangare na bashin
Gwamnatin Tarayya za ta bayar da naira biliyan 265.54 a matsayin gudunmawar cikin gida
Tinubu ya bukaci ‘yan majalisa su gaggauta amincewa da bukatar saboda muhimmancin aikin wajen ci gaban kasa.
Babbar hanyar Sokoto-Badagry na daga cikin mafi girman ayyukan hanyoyi a tarihin Najeriya, inda ake sa ran za ta zama babban ginshikin tattalin arziki tsakanin yankunan Arewa masu albarkatun noma da tashoshin jiragen ruwa na Kudancin kasar.
Ana kuma sa ran aikin zai
Inganta harkokin noma
Saukaka kai kaya zuwa kasuwanni
Bunkasa cinikayya tsakanin yankuna
Jawo jarin masana’antu
Karfafa harkokin gidaje da sufuri
Kara gasa ta tattalin arzikin Najeriya a karkashin yarjejeniyar AfCFTA
Yayin gabatar da rahoton kwamitin kula da basussuka da lamuni, dan majalisa Abdullahi El-Rasheed ya bukaci majalisar ta mara wa bukatar baya, yana mai cewa aikin na da matukar amfani ga ci gaban tattalin arzikin Najeriya.
Add A Comment