Kamfanin Pipeline Infrastructure Nigeria Limited (PINL) ya ce tsaron bututun mai da gas ya zama muhimmin abu wajen cimma burin Najeriya na bunkasa masana’antar gas da kuma jawo sabbin jarin makamashi da darajarsu ta kai biliyoyin daloli.
Kamfanin ya bayyana cewa yawan manyan ayyukan gas da yarjejeniyoyin da ake kulla a kasar ba za su haifar da ci gaban tattalin arziki, samar da ayyukan yi da inganta samar da makamashi ba matukar al’umma, jami’an tsaro da sauran masu ruwa da tsaki ba su hada kai wajen kare muhimman ababen more rayuwa daga lalata da barnatawa.
Babban Manajan Hulda da Al’umma da Masu Ruwa da Tsaki na PINL, Dr Akpos Mezeh, ne ya bayyana hakan a Yenagoa, Jihar Bayelsa, yayin taron masu ruwa da tsaki na kamfanin na watan Agusta 2026.
Mezeh ya ce rattaba hannu kan yarjejeniyar Intergovernmental Agreement kan aikin African Atlantic Gas Pipeline (AAGP) da shugabannin kasashen ECOWAS suka yi ya bude sabon babi na hadin gwiwar makamashi a yankin, tare da kara nuna muhimmancin albarkatun gas na Najeriya.
Aikin AAGP, wanda aka tsara zai kai tsawon kilomita 6,900, zai hada Najeriya da Morocco ta wasu kasashe 13 na gabar Tekun Atlantika, tare da samar da hanyar isar da gas zuwa wasu kasashen Sahel da ba su da mashigin teku.
Ana sa ran bututun zai rika jigilar kusan mita biliyan 30 na iskar gas a duk shekara.
A cewar Mezeh, aikin zai taimaka wajen inganta tsaron makamashi a yankin, bunkasa masana’antu, samar da ayyukan yi da kuma karfafa alakar kasuwannin makamashi na Yammacin Afirka da Turai.
Ya ce wannan ci gaba ya kamata ya zama darasi ga al’ummomin da ke karbar bakuncin ayyukan makamashi cewa tsaron ababen more rayuwa na makamashi yana da alaka kai tsaye da makomar tattalin arzikin Najeriya.
Mezeh ya ce, “Manyan ababen more rayuwa na makamashi ba za su samu damar bunkasa ba idan ba a samu tsaron bututun mai da gas, zaman lafiya a tsakanin al’umma da hadin kan masu ruwa da tsaki ba.”
Ya kuma bayyana cewa karuwar zuba jari a bangaren gas na Najeriya ya kara muhimmancin kare bututun gas da sauran kayayyakin more rayuwa da ke kai makamashi zuwa masana’antu, tashoshin samar da wutar lantarki da wuraren fitar da kayayyaki zuwa kasashen waje.
Mezeh ya kuma ambaci wasu alkaluman NNPC Limited, inda ya ce kamfanin ya samu ribar bayan haraji ta N535bn a watan Yuni 2026, idan aka kwatanta da N462bn da ya samu a watan Mayu.
Ya kara da cewa kudaden shiga na wata-wata sun kai kusan N4.39tn, yayin da gudummawar da bangaren mai da gas ya bayar zuwa Asusun Tarayya tsakanin watan Janairu da Yuni ta kai N6.286tn.
A cewarsa, samar da iskar gas ya karu zuwa kusan biliyan 7.84 na standard cubic feet a kowace rana, yayin da samar da danyen mai ya dan ragu zuwa ganga miliyan 1.72 a kowace rana sakamakon wasu matsalolin aiki da fasaha.
A bangaren manyan ayyukan gas, Mezeh ya ce aikin Obiafu-Obrikom-Oben (OB3) Gas Pipeline ya kai kashi 98 cikin 100 na kammalawa, inda ake gudanar da ayyukan hada shi da sauran hanyoyin bututun gas kafin fara samar da iskar gas.
Ya ce aikin Ajaokuta-Kaduna-Kano (AKK) Gas Pipeline shi ma ya kai kashi 94 cikin 100 na kammalawa, yayin da aka kaddamar da ANOH Gas Processing Plant.
Ya kara bayyana cewa NNPC Limited ta samu yarjejeniyoyin sayarwa da sayen gas da darajarsu ta haura dala biliyan 20 a cikin shekara guda da ta gabata.
Yarjejeniyoyin sun hada da samar da biliyan 1.29 na standard cubic feet na gas a kowace rana domin ciyar da masana’antun LNG na dogon lokaci, da kuma karin biliyan 750 na standard cubic feet a kowace rana domin samar da gas ga masana’antun cikin gida.
Mezeh ya ce wadannan yarjejeniyoyi, tare da ayyukan da suka shafi Dangote Refinery, UTM FLNG da Ajaokuta Steel Company, za su iya kara bunkasa masana’antu, inganta tsaron makamashi da samar da ayyukan yi.
Sai dai ya yi gargadin cewa wadannan fa’idodi na iya shiga hadari idan aka ci gaba da samun lalata bututun mai da gas, satar danyen mai da kuma ayyukan zagon kasa.
Ya bayyana cewa ayyukan da ake gudanarwa a hanyoyin Trans Niger Pipeline da Eastern Gas Network sun samu ci gaba a watan da ya gabata sakamakon hadin gwiwar PINL, jami’an tsaro, ‘yan kwangila da al’ummomin da ke karbar bakuncin ayyukan.
Duk da haka, ya amince cewa an samu wasu yunkurin lalata bututun mai, zagon kasa da kuma lalacewar kayan aiki a wasu wurare, inda aka dauki matakan gaggawa domin gyara matsalolin, yayin da aka kama wasu da ake zargi kuma ake ci gaba da gudanar da bincike.
Shugaban PINL ya yi kira da a kara karfafa sa ido daga al’umma tare da hanzarta isar da bayanan sirri ga jami’an tsaro.
Ya ce, “Duk wani rahoto da aka bayar cikin lokaci da kuma kowane irin taka-tsantsan da aka yi na kare rayuka, muhalli da tattalin arzikin Najeriya ne.”
Kamfanin ya kuma sanar da cewa taron masu ruwa da tsaki zai koma gudanarwa duk bayan watanni biyu maimakon kowane wata, domin ba wa mahukunta karin lokaci wajen aiwatar da shawarwarin da aka cimma a tarukan.
Sai dai Mezeh ya tabbatar da cewa PINL zai ci gaba da tuntubar al’ummomin da ke karbar bakuncin ayyukansa tare da magance matsalolin gaggawa a duk lokacin da suka taso.
Ya kuma bayyana cewa kamfanin ya amince da mayar da shirin bayar da tallafin karatu ga daliban al’ummomin da ke karbar bakuncin ayyukansa ya zama shiri na shekara-shekara har zuwa karshen kwangilar kamfanin da Gwamnatin Tarayya.
Baya ga tallafin karatu, kamfanin zai ci gaba da shirye-shiryen tallafa wa matasa da mata, koyar da sana’o’i, bunkasa kananan ‘yan kasuwa, sa ido na al’umma da kuma hanyoyin warware rikice-rikice cikin lumana.
Taron ya samu halartar sarakunan gargajiya, shugabannin al’umma, wakilan matasa da mata, jami’an tsaro, jami’an gwamnati, wakilan NNPC Limited da sauran masu ruwa da tsaki.
Mezeh ya bukaci dukkan masu ruwa da tsaki da su yi watsi da lalata bututun mai da gas da kuma satar danyen mai, yana mai jaddada cewa kare muhimman ababen more rayuwa na kasa nauyi ne da ya rataya a wuyan kowa.
Ya ce manufar ba wai kare bututun mai da gas kadai ba ce, illa kuma samar da yanayin da zai ba da damar zuba jari ya bunkasa, al’umma su amfana da damar tattalin arziki, sannan Najeriya ta cimma cikakken amfani da albarkatun gas dinta.
