Najeriya da Masarautar Lesotho sun sake jaddada aniyarsu ta ƙarfafa alaƙar ƙasashen biyu ta hanyar faɗaɗa kasuwanci, zuba jari, fasaha, makamashi mai sabuntawa da haɗin gwiwar kamfanoni masu zaman kansu domin bunƙasa tattalin arziki da ƙarfafa haɗin kan tattalin arzikin Afirka.
An bayyana hakan ne a taron Nigeria–Lesotho Executive Investment Forum da aka gudanar a Abuja, inda jami’an gwamnati, shugabannin kamfanoni da masu zuba jari daga ƙasashen biyu suka tattauna hanyoyin samar da haɗin gwiwar kasuwanci a ƙarƙashin yarjejeniyar AfCFTA.
Firaministan Lesotho, Sam Matekane, wanda ya jagoranci tawagar ƙasarsa, ya ce ziyarar ta su na da nufin ƙarfafa dangantakar da ke akwai, samar da sabbin damar zuba jari da kuma gabatar da Lesotho a matsayin ƙasa mai jan hankalin masu zuba jari.
Ya bayyana cewa gwamnatin Lesotho na aiwatar da sauye-sauye domin bunƙasa masana’antu, inganta ababen more rayuwa, samar da ayyukan yi da kuma ƙarfafa tattalin arzikin da kamfanoni masu zaman kansu ke jagoranta.
Matekane ya tabbatar wa masu zuba jari cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da samar da yanayin kasuwanci mai gaskiya da kwanciyar hankali domin jawo hankalin masu zuba jari na cikin gida da na ƙasashen waje.
Ya bayyana fannoni kamar masana’antu, gine-gine, yawon buɗe ido, baƙunci, makamashi mai sabuntawa, fasahar zamani da masana’antun ƙara darajar kayayyaki a matsayin manyan wuraren da ke ɗauke da damar zuba jari.
Firaministan ya kuma ƙarfafa matasa ‘yan kasuwa su rungumi haƙuri, jajircewa da gaskiya maimakon neman arziki cikin gaggawa, yana mai cewa nasara tana zuwa ne ta hanyar aiki tuƙuru da dagewa.
A nasa jawabin, wakilin Shugaban Abuja Chamber of Commerce and Industry (ACCI), Aliyu Idi Hong, ya ce lokaci ya yi da ƙasashen Afirka za su daina mayar da hankali kan ƙalubalen kasuwanci a tsakaninsu, su fi karkata wajen gina haɗin gwiwar da za ta samar da ci gaba.
Shi ma Mawallafin African Leadership Magazine, Ken Giami, ya ce Najeriya na da babbar kasuwa, yayin da Lesotho ke da damammakin zuba jari masu yawa, yana mai cewa haɗin gwiwar ƙasashen biyu zai taimaka wajen bunƙasa tattalin arzikin Afirka.
An kammala taron da zaman haɗa kamfanonin Najeriya da na Lesotho domin tattauna damar kasuwanci, inda mahalarta suka bayyana fatan cewa hakan zai haifar da sabbin yarjejeniyoyin zuba jari da ƙarfafa haɗin gwiwar tattalin arziki tsakanin Yammacin da Kudancin Afirka.
