Wata kungiya ta yi kira ga daukacin ‘yan Najeriya da su hada kai domin magance matsalolin tsaro da ke addabar kasar nan, tana mai cewa matsalar ta shafi kowa ba tare da la’akari da bambancin siyasa, addini ko kabila ba.
A cewar sanarwar kungiyar, tafiyar lumana da ake shirin gudanarwa za ta zama wata hanya ta karfafa hadin gwiwa tsakanin al’umma, sarakuna, malamai, shugabannin al’umma da ‘yan siyasa wajen nemo mafita ga matsalar tsaro.
Sanarwar ta bayyana cewa matsalar rashin tsaro ta fara ne da tayar da kayar bayan Boko Haram a Arewa maso Gabas, amma daga baya ta fadada zuwa fashi da makami, garkuwa da mutane, rikicin makiyaya da manoma da sauran laifuffuka a sassa daban-daban na kasar.
Kungiyar ta jaddada cewa ‘yan ta’adda da masu garkuwa da mutane ba sa bambancewa tsakanin mutane, domin hare-harensu na shafar mutane daga kowane bangare na siyasa, addini da kabila.
Ta bukaci shugabannin siyasa daga dukkan jam’iyyu da su ajiye bambance-bambancen siyasa tare da hada kai domin magance matsalar tsaro.
Haka kuma kungiyar ta yi kira ga tsoffin shugabannin kasa, tsoffin hafsoshin soja, masu rike da mukaman gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki da su bayar da gudunmawar shawarwari da kwarewarsu wajen samar da mafita mai dorewa.
Ta kuma bukaci shugabannin addinai su kara wayar da kan jama’a kan zaman lafiya, hakuri da mutunta rayuwar dan Adam tare da yin tir da ta’addanci, garkuwa da mutane da duk wani nau’in tashin hankali.
Kungiyar ta yi kira ga al’ummomi su kasance masu sanya ido tare da taimaka wa hukumomin tsaro wajen gano masu aikata laifuffuka.
A karshe, ta gargadi ‘yan Najeriya da kada su mayar da matsalar tsaro batun siyasa, tana mai cewa kare rayuka da dukiyoyin jama’a ya kamata ya fi kowace manufa ta siyasa muhimmanci. Ta kuma jaddada cewa gwamnati kadai ba za ta iya kawo karshen matsalar tsaro ba tare da hadin kan jama’a ba.
