Dakarun rundunar Sojojin Najeriya ta Brigade ta 12 sun ceto wasu mutane biyu da aka yi garkuwa da su, bayan sun gaggauta kai dauki a wani harin sace mutane da ya faru a Egbe, cikin Karamar Hukumar Yagba West ta Jihar Kogi.
An ceto matar da jaririnta mai watanni shida ne bayan sojoji suka kaddamar da binciken neman wadanda aka sace, bayan an sace mambobi biyar na wata iyali a yankin.
Lamarin ya faru ne da daddare a ranar Laraba, inda wasu da ake zargin ‘yan ta’adda suka kutsa cikin wani gida kusa da Makarantar Solid Rock da ke Ijalu, Egbe, suka yi awon gaba da mutanen.
A cewar rundunar sojojin, dakarun sun hada kai da ‘yan Vigilante Group of Nigeria (VGN) domin gaggauta bin sawun masu garkuwa da mutanen.
Matsin lamba daga hadin gwiwar jami’an tsaro ya tilasta wa masu garkuwar barin matar da jaririnta a yankin Oro kafin su tsere zuwa cikin dazuka.
An mika wadanda aka ceto cikin lafiya ga iyalansu, yayin da ake ci gaba da bincike domin ceto sauran wadanda aka sace da kuma kama wadanda suka aikata laifin.
A cikin wata sanarwa daga Mataimakin Daraktan Yada Labarai na Brigade ta 12, Laftanar Hassan Abdullahi, ya ce an gudanar da aikin ne bayan samun kiran gaggawa daga al’ummar yankin.
Ya ce dakarun sun kuma ceto fasinjoji 23 a wani aikin ceto da aka gudanar a hanyar Ayegunle–Bunu a Karamar Hukumar Kabba-Bunu a ranar 1 ga watan Yuni.
Haka kuma, a ranar 30 ga Mayu, dakarun sun dakile wani yunkurin sace mutane a Lokoja tare da kashe wani dan ta’adda a yayin farmaki.
Sojojin Najeriya sun jaddada aniyarsu ta kare rayuka da dukiyoyin jama’a, tare da yin kira ga al’umma da su rika ba da bayanai masu inganci ga jami’an tsaro cikin lokaci.
