Darakta Janar kuma Babban Jami’in Hukumar Kula da Harkokin Wasanni ta Kasa (NIS), Kwamared Philip Shaibu, ya yabawa tawagar Super Eagles, masu horas da su da kuma Babban Mataimaki na Musamman ga Shugaban Kasa kan Raya Wasannin Matasa, Hon. Adeyinka Anthony Adeboye, bisa yadda suka taka rawar gani a gasar Unity Cup da kuma wasan sada zumunta da kasar Poland.
Shaibu, wanda ya halarci taron kallon wasan Najeriya da Poland a filin wasa na Moshood Abiola da ke Abuja, ya ce ‘yan wasan sun nuna jajircewa, kwarewa da kuma ruhin gwagwarmaya da ya sanya kwallon kafar Najeriya ta samu karbuwa a duniya.
Tsohon Mataimakin Gwamnan Jihar Edo ya bayyana cewa gasar Unity Cup da wasan Poland sun nuna yadda wasanni ke hada kan al’umma tare da inganta hadin kai, alfaharin kasa da kyautata dangantaka tsakanin kasashe.
Ya kuma yabawa Adeboye saboda kokarinsa na bunkasa wasannin matasa a matakin kasa, yana mai cewa hakan ya yi daidai da manufar gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta Renewed Hope Agenda wajen samar wa matasa damammaki da karfafa hadin kai.
Shaibu ya ce:
“Super Eagles sun cancanci yabo saboda yadda suka wakilci Najeriya da mutunci. Haka kuma ina taya masu horaswa da Hon. Adeyinka Adeboye murna bisa gudunmawar da suke bayarwa wajen daukaka martabar wasannin Najeriya.”
Sai dai ya gargadi ‘yan wasan da su rika mai da hankali har zuwa karshen wasa, yana mai nuni da cewa Najeriya ta kusa samun nasara a wasan da Poland bayan kwallon fenariti da Paul Onuachu ya ci kafin Poland ta rama a karshen wasa.
Ya ce:
“Kwallon kafa wasa ne na minti 90 da ma karin lokaci. Dole ne ‘yan wasa su kasance cikin shiri da mayar da hankali har zuwa busar karshe. Kuskure kadan na iya sauya sakamakon wasa.”
Shaibu ya bukaci tawagar Super Eagles da su dauki wasan a matsayin darasi domin ci gaba da gina kungiyar da za ta iya fafatawa da manyan kasashen duniya.
Ya kuma bayyana kwarin gwiwarsa cewa makomar kungiyar na da kyau, tare da kira ga ‘yan Najeriya su ci gaba da mara wa Super Eagles baya a wasanninsu na gaba.
