Ƙungiyar likitoci a jihar Ondo sun ƙara matsa lamba kan gwamnati kan batun rashin kyakkyawan walwala da tabarbarewar harkar kiwon lafiya a jihar, inda suka sake jaddada barazanar tsunduma yajin aiki idan ba a ɗauki mataki cikin gaggawa ba.
Shugaban NMA na jihar, Dr Abel Alonge, ya bayyana cewa yawan likitoci a Ondo ya ragu da kusan rabin abin da aka saba da shi a baya, duk da ƙaruwa yawan jama’a, lamarin da ya jefa asibitoci cikin matsanancin ƙarancin ma’aikata.
Ya ce wannan yanayi ya sa wasu asibitocin gwamnati ke aiki da likita ɗaya ko kuma babu ko ɗaya, abin da ke tilasta wa sauran ma’aikatan aiki a ƙarƙashin matsin lamba da gajiya mai tsanani.
Ƙungiyar ta kuma yi nuni da cewa kayan aiki a yawancin asibitoci sun tsufa matuƙa, inda wasu ke amfani da na’urori da suka kai shekaru 10 zuwa 20 ba tare da sabuntawa ba.
Sun kuma zargi gwamnatin jihar da rashin biyan ma’aikata albashi mai kyau, lamarin da ya sa likitoci ke barin jihar zuwa Lagos, Ogun, Ekiti da Osun domin neman ingantacciyar albashi da yanayin aiki.
A cewarsu, idan gwamnati ta gaza ɗaukar matakan gaggawa cikin wa’adin da suka bayar, za su shiga yajin aiki wanda zai iya durƙusar da harkar kiwon lafiya a jihar.
