Rundunar ‘yan sanda ta jihar Edo ta ce jami’anta sun ceto wata mata mai suna Mrs Vivian George, mai shekaru 57, bayan wani samame da suka gudanar a dazukan Igbanke tare da haɗin gwiwar ƙungiyoyin tsaro na gida.
Wata sanarwa daga mai magana da yawun rundunar, ASP Eno Ikoedem, ta bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar 16 ga Mayu, 2026, lokacin da ‘yan bindiga suka sace matar tare da ɗanta, Chinedu George mai shekaru 18, yayin da suke kan hanyar zuwa gona a yankin Ottah Community.
Rahotanni sun nuna cewa matashin ya samu damar tserewa daga hannun masu garkuwar, inda ya kai rahoto ga hukumomin tsaro.
Bayan samun rahoton, jami’an ‘yan sanda tare da haɗin gwiwar Edo State Security Corps da kuma mafarauta suka shiga daji domin gudanar da aikin ceto.
Sanarwar ta ce an samu musayar wuta tsakanin jami’an tsaro da masu garkuwar, inda ‘yan bindigar suka tsere cikin daji bayan da aka matsa musu lamba, wasu kuma sun samu raunin harbin bindiga.
A ƙarshe, an samu nasarar ceto matar ba tare da rauni ba, sannan aka mika ta ga iyalanta cikin koshin lafiya.
Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, CP Monday Agbonika, ya yaba wa jami’an tsaro bisa ƙwazon da suka nuna, tare da jaddada aniyar rundunar na ci gaba da yaki da garkuwa da mutane da sauran laifuka a jihar Edo.
