Mazauna yankin Ikot Okpok da ke cikin ƙaramar hukumar Ikot Abasi a jihar Akwa Ibom sun koka kan lalacewar wata muhimmiyar hanya da suka ce ta zama babban cikas ga harkokin ilimi da rayuwar yau da kullum.
Rahotanni sun nuna cewa hanyar da ta ratsa garuruwa da dama ciki har da Atan Ikpe, Ikot Efre, Ikot Okpok, Ikot Alkpabio, Atan Ekaiko da Ikot Etenge Ndon, ta lalace matuƙa bayan kamfanin da ke aikin gina ta ya dakatar da aiki.
Wani mazaunin yankin kuma tsohon malami, Bassey Ukpong, ya ce lalacewar hanyar na hana ɗalibai zuwa makaranta musamman a lokacin damina, lamarin da ke ƙara yawan yaran da ba sa zuwa makaranta.
Ya kuma bayyana cewa matsalar ta shafi zirga-zirgar jama’a zuwa gonaki, coci-coci da sauran muhimman wurare.
Mazauna yankin sun ce an bayar da kwangilar aikin ne tun a shekarar 2019 a gwamnatin tsohon gwamna Udom Emmanuel, amma aikin bai kammala ba duk da sakin wasu kuɗaɗe daga gwamnatin yanzu ta Gwamna Umo Eno.
Sun zargi masu aikin da yin ginin da bai kai ƙa’ida ba, inda aka ce an ɗora wasu mutane da ba su da ƙwarewa a aikin, lamarin da ya ƙara janyo matsaloli ga al’umma.
Sarkin ƙauyen Ikot Okpok, Cif Iko-Abasi Alfred Ekiko, ya ce dalibai, malamai, mata da matasa na fuskantar wahala sosai saboda halin da hanyar ke ciki.
Ya yi kira ga Gwamna Umo Eno da ya sa baki tare da umartar kamfanin da ke aikin ya koma wurin domin kammala aikin.
Shi ma wani jagoran al’umma, Elder Ntudo Udoessien, ya bayyana cewa direbobi da dama sun daina amfani da hanyar saboda tsoron lalacewar motocinsu.
Da aka tuntubi Kwamishinan Ayyuka na jihar, Farfesa Eno Ibanga, ya ce zai tuntubi injiniyan aikin domin samun cikakken bayani kan halin da aikin yake ciki da kuma matakan da za a ɗauka.
