Hukumar kiyaye afkuwar hadura ta kasa (FRSC) ta ja kunnan direbobi dangane da gudun wuci sa’a da suke a kan tituna musamman manyan titunan Najeriya.
Haka kuma hukumar ta bukaci Direbobin da su guji ketare mota wato Overtaking a titunan, wanda hakan ne zai sa a rage yawan samun asarar rayukan al’umma da ake samu sanadiyyar hatsari a manyan titunan na Najeriya.
Dr Samuel Ibitoye, shugaban hukumar ta FRSC a jihar ta Ondo ne ya bayyana hakan a garin Ore dake karamar hukumar Odigbon jihar ta Ondo, sakamkon wani hadari da aka samu a ranar Asabar 01/02/2025 wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 28.
Ibitoye ya Kuma bayyanawa kamfanin dillancin labarai na kasa NAN cewa mutane 30 ne hadarin ya rutsa da su sakamakon tawo mugama da wasu motoci sukai a kan titin na Ore wanda yai sanadiyyar mutuwar mutanan 28.
Ya kuma shawarci direbobi da su rinka bin dokokin tuki yadda ya kamata musamman a manyan titunan kasar nan.
A cewar sa fasinjojima suna da hakkin a kaisu inda sukeso ba tare da wani abu ya samesu ba.
