Gwamnatin Jihar Oyo ta tabbatar wa mazauna jihar cewa tana cikin cikakken shiri domin hana yaduwar cutar Ebola tare da gano duk wata alamar bullar cutar cikin gaggawa.
Wannan tabbacin ya biyo bayan rahotannin bullar cutar a Jamhuriyar Dimokuradiyyar Kongo da kuma tabbatar da wasu masu dauke da cutar a kasar Uganda.
Kwamishinar Lafiya ta jihar, Dakta Oluwaserimi Ajetunmobi, ta bayyana cewa duk da cewa ba a samu wani mutum da ke dauke da cutar Ebola a Najeriya ba, gwamnatin jihar na sa ido sosai kan halin da ake ciki tare da daukar matakan kariya da shiri domin kare lafiyar al’umma.
Ta ce an kara karfafa tsarin sa ido kan cututtuka a dukkan kananan hukumomi 33 na jihar, yayin da aka sanya cibiyoyin lafiya cikin shirin ko-ta-kwana domin daukar matakin gaggawa idan bukatar hakan ta taso.
A cewarta, an kuma tura jami’an sa ido kan cututtuka, kungiyoyin bayar da agajin gaggawa, dakunan gwaje-gwaje da sauran muhimman sassan da ke da alhakin dakile barkewar cututtuka.
Dakta Ajetunmobi ta bukaci ma’aikatan lafiya, shugabannin addinai da na gargajiya, da kuma al’umma gaba daya su kasance cikin shiri tare da kai rahoton duk wanda ya nuna alamomin cutar kamar zazzabi mai tsanani, amai, gudawa, kasala ko zubar jini ba tare da wani bayani ba.
Ta jaddada cewa babu wani tabbataccen mutum da aka samu da cutar Ebola a Jihar Oyo ko Najeriya baki daya, tare da kira ga jama’a da su guji firgici, su ci gaba da bin ka’idojin kariyar lafiya.
Gwamnatin jihar ta kuma tabbatar da ci gaba da hadin gwiwa da Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya, Hukumar NCDC, Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) da sauran abokan hulda domin tabbatar da kare lafiyar al’umma.
