Hukumar kula da masu yi wa kasa hidima ta kasa (NYSC) a jihar Gombe ta bayyana cewa akwai masu bautar kasa biyu da za su sake maimaita shekarar hidimarsu, yayin da wasu biyu kuma aka kara musu wa’adin hidima na watanni hudu sakamakon wasu matsaloli da suka shafi aikin hidimar kasa.
Kodinetar NYSC a jihar, Chinwe Nwachuku, ce ta bayyana hakan a ranar Alhamis yayin bikin yaye masu bautar kasa na rukuni na 2025 Batch ‘A’ Stream II da aka gudanar a sakatariyar karamar hukumar Gombe.
Ta bayyana cewa jimillar masu bautar kasa 901 ne suka kammala hidimarsu cikin nasara a jihar, wadanda suka hada da maza 503 da mata 398.
“Akwai masu bautar kasa biyu da za su maimaita hidima, yayin da wasu biyu aka kara musu wa’adin hidima na watanni hudu,” in ji ta.
An samu dan rudani a wajen bikin bayan wata saniya ta kutsa cikin wurin taron, inda ta kusa jikkata wasu masu bautar kasa da ke zaune karkashin bishiya, sai dai babu wanda ya samu rauni.
Nwachuku ta yaba wa masu bautar kasar da suka kammala hidima bisa jajircewa da kuma gudummawar ayyukan ci gaban al’umma da suka bayar a lokacin hidimarsu.
Ta ce shekara guda da ta gabata sun amsa kiran kasa tare da fuskantar kalubale da kuma samun sabbin kwarewa da damammaki.
Ta kuma bukace su da su yi amfani da ilimin sana’o’i da suka samu karkashin shirin Skill Acquisition and Entrepreneurship Development domin dogaro da kai.
Har ila yau, ta gargade su da su guji yin tafiya da dare da kuma shiga ayyukan da za su bata sunan shirin NYSC.
Daga bisani, ta ayyana shekarar hidimar 2025 Batch ‘A’ Stream II a hukumance a matsayin wacce aka kammala.
