Mahukuntan Iran sun gudanar da manyan bukukuwan aure a bainar jama’a a Tehran domin ma’auratan da suka shiga wani shirin gwamnati na nuna shirinsu na sadaukar da rayukansu a yakin da kasar ke yi da Amurka da Isra’ila.
An gudanar da bukukuwan ne a daren Litinin a manyan dandamali da filayen taro daban-daban a babban birnin kasar, ciki har da filin Imam Hossein da ke tsakiyar Tehran, inda sama da ma’aurata 100 suka halarta.
Kafafen yada labaran gwamnatin Iran sun nuna bukukuwan kai tsaye a talabijin domin kara wa jama’a kwarin gwiwa yayin da ake ci gaba da fuskantar barazanar sake barkewar yaki daga Amurka.
Rahotanni sun bayyana cewa ma’auratan sun shiga wani shiri da ake kira “janfada” a harshen Persian, wanda ke nufin shirye-shiryen sadaukar da kai domin kare kasa, ciki har da kafa garkuwar mutane a kusa da cibiyoyin lantarki da sauran wurare masu muhimmanci.
Mahukuntan Iran sun ce miliyoyin mutane sun riga sun sanya sunayensu a cikin shirin, ciki har da shugaban kasar, Masoud Pezeshkian, da shugaban majalisar dokoki, Mohammad Bagher Ghalibaf.
Hotunan da kafar AFP ta wallafa sun nuna yadda ma’auratan suka isa wurin taron cikin motocin soji masu dauke da bindigogi, yayin da wani malami ya jagoranci daurin auren a kan wani babban dandali da aka kawata da hoton sabon Jagoran Addini na Iran, Mojtaba Khamenei.
Wata amarya sanye da farin hijabi ta bayyana cewa duk da yakin da ake fama da shi, matasa na da hakkin yin aure da ci gaba da rayuwa.
