Wani ma’aikaci a Hukumar Securities and Exchange Commission (SEC), Bagudu Mohammed Waziri, ya fara bayar da gudummawar N10,000 duk wata ga Nigeria Police Trust Fund da kuma Armed Forces Trust Fund har zuwa lokacin da zai yi ritaya.
A wata wasika da ya rubuta ranar 15 ga Afrilu, 2026 zuwa ga Akanta Janar na Tarayya, Waziri ya ce matakin nasa ya samo asali ne daga abin da Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi na bayar da albashinsa gaba ɗaya domin tallafawa jami’an tsaro.
Wasikar, mai taken “Donation In Support Of The Nigerian Police Trust Fund and the Armed Forces Trust Fund”, ta kuma isa ga Ministan Kudi, Babban Hafsan Tsaro, da kuma Sufeto Janar na ‘Yan Sanda.
Waziri ya bayyana cewa zai rika cire N10,000 daga albashinsa kowane wata ga kowanne daga cikin asusun biyu, domin taimakawa jami’an tsaro da ke sadaukar da rayuwarsu wajen kare ƙasa.
Ya kuma yi kira ga ‘yan Najeriya masu kishin ƙasa da su bada irin wannan gudummawa, yana mai cewa ƙananan taimako daga jama’a na iya zama babbar gudummawa wajen rage matsalolin kuɗi da hukumomin tsaro ke fuskanta.
Ya ce, “Idan kowa ya bada tasa gudummawar, za mu iya samar da isasshen tallafi domin inganta tsaro da kare rayuka da dukiyoyi a ƙasa.”
Haka kuma ya bukaci a ba shi cikakkun bayanan asusun domin a fara cire kudin kai tsaye daga albashinsa kafin a biya shi
