Wacce ta kafa TOS Foundation Africa kuma Shugabar Kamfanin TOS Group, Chief Osasu Igbinedion Ogwuche, ta shiga jerin manyan shugabanni 27 daga fadin nahiyar Afirka da aka zaba domin shirin Tutu Fellowship Programme na shekarar 2026.
An gudanar da zaben ne ta hanyar gasa mai tsauri wadda ta ja hankalin dubban sunaye da aka gabatar daga kasashen Afirka daban-daban, inda aka zabo wadanda suka fi nuna kwarewa a shugabanci da hidimar al’umma.
Zaben nata ya nuna irin rawar da take takawa a fannin shugabanci, gina tsare-tsare, da kuma bunkasa kyakkyawan mulki a Najeriya da sauran kasashen Afirka.
A karkashin jagorancinta, TOS Group ya zama kamfani mai fadin ayyuka daban-daban da suka hada da harkokin kafofin yada labarai, agaji, gidaje, yawon shakatawa da makamashi. Daga cikin rassan kamfanin akwai TOS TV Network, TOS Foundation Africa, NatSu Global, Lezeanoo Services Ltd., da kuma NOLA Restaurant and Lounge.
Shirin Tutu Fellowship, wanda African Leadership Institute ke jagoranta, ana daukarsa a matsayin daya daga cikin manyan shirye-shiryen horar da shugabanni a nahiyar Afirka, wanda ke gano tare da tallafawa shugabanni masu tasiri a fannoni daban-daban.
A cikin sanarwar da aka fitar, kungiyar ta ce:
“Wadannan sabbin membobi suna nuna zurfin kwarewar shugabanci a Afirka, kuma shirin yana ci gaba da karfafa su domin su zama masu kawo sauyi mai amfani a nahiyar.”
Wakilin sadarwa na TOS Group, Hammed Adejare, ya bayyana cewa wannan karramawa na nuna irin kima da gudummawar da shugabar ke bayarwa wajen bunkasa shugabanci mai nagarta da tsari mai dorewa.
