Fitacciyar jarumar Nollywood kuma mai shirya fina-finai, Funke Akindele, ta bayyana jerin fitattun jaruman da za su fito a sabon fim ɗinta mai suna “The Four: No One Fights Alone.”
An shirya fara nuna fim ɗin a gidajen sinima a faɗin duniya daga ranar 11 ga Disamba, 2026.
Fim ɗin ya tattaro wasu daga cikin manyan jaruman Nollywood, tare da fitattun mawaka da wasu daga cikin masu tasiri a harkar nishaɗi.
Daga cikin jaruman da za su fito a fim ɗin akwai Funke Akindele da kanta, Waje, Chioma Akpotha, Bisola Aiyeola, John Ekanem, Wunmi Toriola, Lateef Adedimeji, Ireoluwa Olaniyan, Ali Nuhu, Omotunde Adebowale David wanda aka fi sani da Lolo1, Mide Iwasokun, Kolapo Omotosho, Shoday, Richard Mofe-Damijo, Timini Egbuson, Uzor Arukwe da Ogbolor.
Haka kuma fim ɗin zai ƙunshi Ronke Oshodi Oke, Antar Laniyan da wasu fitattun mutane a fannin nishaɗi kamar Samuel Banks da Ayomide Iwasokun.
“The Four” fim ne mai cike da motsin rai, wanda ya ta’allaka ne kan abota, uwa, juriyar rayuwa da kuma ƙarfin gwiwar mata talakawa wajen fuskantar ƙalubalen rayuwa.
Ana sa ran fim ɗin zai kasance cikin fina-finan Nollywood da za su ja hankalin masoya a lokacin da aka fara nuna shi a gidajen sinima a watan Disamba.
