Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    Najeriya Ta Kai Dala $18.4 Biliyan a Cinikayyar Cikin Afirka a 2024

    June 28, 2025

    Afreximbank Ta Ba Najeriya Tallafin $50 Biliyan Don Manyan Ayyuka

    June 28, 2025

    Mutane 28 sun mutu sakamakon gudun wuce sa’a a jihar Ondo- FRSC

    February 2, 2025

    📰 Labarin Yanar Gizo (Hausa Version): Kaduna Pilgrims Board Ya Tabbatar An Yi Hadaya Ga Duk Masu Biyan Kuɗi

    June 9, 2026

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Zafin Rana Mai Tsanani Ya Ɓarke a Turai: Matsalar Heat Dome

    June 30, 2025

    Taraba Ta Gargadi Jama’a Kan Biyan Haraji a Asusun Banki Na Gwamnati Kadai

    June 11, 2026

    Kotun Ta Tabbatar Da ‘Yancin Indigene Ga ‘Ya’yan Dan Kabilar Hausa A Jos North

    June 11, 2026

    TikTok Ta Cire Bidiyo Miliyan 4 A Najeriya, Ta Dakatar da LIVE 86,000

    June 9, 2026

    Kotun Los Angeles Ta Wanke Kristina Khorram Daga Zargin Safarar Jima’i

    June 9, 2026
  • Asrah 24 TV
  • Education

    NANS Ta Bukaci A Sanya Wakilan Dalibai Cikin Kwamitin Yaki da Ebola

    June 10, 2026

    JAMB Ta Bude Shafin Fitar Da Takardun Jarabawar Mop-Up UTME Ta 2026

    June 8, 2026

    Sojojin Najeriya Sun Yaye Sabbin Paratroopers Bayan Kammala Horon Tsalle Daga Jirgin Sama

    June 5, 2026

    Achievers University Ta Bankado Zargin Damfarar Kudin Makaranta Ta N457.5m

    May 25, 2026

    NYSC ta shawarci iyaye su taimaka wa ‘ya’yansu da karin kudin tafiya

    May 21, 2026
  • Health

    Gwamnati Ta Bukaci Mata Masu Juna Biyu Su Rika Zuwa Asibiti Tun Da Wuri Domin Kula Da Lafiyarsu

    June 11, 2026

    PCN Ta Cafke Mutane Biyar Kan Karya Hatimin Shagunan Magunguna Ba Bisa Ka’ida Ba A Kano

    June 11, 2026

    FCTA Ta Kaddamar Da Sabuwar Hanyar Maganin Fibroid Ba Tare Da Tiyata Ba, Za Ta Yi Wa Mata 100 Magani Kyauta

    June 11, 2026

    Jihar Neja Ta Kaddamar Da Hukumar Kula Da Asibitocin Masu Zaman Kansu

    June 8, 2026

    OYO TA KWANTAR WA MAZAUNA HANKALI KAN CUTAR EBOLA, TA SA MA’AIKATAN LAFIYA CIKIN SHIRI

    June 4, 2026
  • Podcast
  • Politics

    APC Na Tsoron Karfin Accord A Fadin Osun

    June 12, 2026

    Wasu ‘Yan Najeriya Na Ba ‘Yan Ta’adda Abinci Da Bayanai – Ministan Tsaro

    June 12, 2026

    Majalisar Wakilai Ta Nada Fred Agbedi Sabon Jagoran ‘Yan Adawa

    June 12, 2026

    Agbedi Ya Zama Sabon Jagoran ‘Yan Adawa A Majalisar Wakilai, Soro Da Dasuki Sun Samu Mukamai

    June 11, 2026

    Dan Majalisar Bayelsa, Frederick Agbedi, Ya Zama Sabon Jagoran ‘Yan Adawa A Majalisar Wakilai

    June 11, 2026
  • Sports

    Messi Shi Ne Mafi Kyawun Dan Wasa Da Na Taba Gani

    June 12, 2026

    Serena Williams Ta Dakatar Da Komawarta Bayan Raunin Abokiyar Wasanta Mboko

    June 11, 2026

    Michel Platini Ya Kai Kara FIFA da Shugabanta Gianni Infantino Kan Zargin Rashawa

    June 9, 2026

    Comoros Ta Tsallaka Wasa Da Super Falcons Bayan Doke Sudan 30–0

    June 9, 2026

    Messi Zai Koma Fili Yayin Da Argentina Ke Kammala Shirye-shiryen Kofin Duniya Na 2026

    June 9, 2026
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home » Sammacin Kama Da Majalisa Ta Bayar Ya Ba Ni Mamaki, Ina Jinya A Kasar Waje — Mele Kyari
Politics

Sammacin Kama Da Majalisa Ta Bayar Ya Ba Ni Mamaki, Ina Jinya A Kasar Waje — Mele Kyari

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaJune 11, 20262 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp
images 2026 06 11T120149.504 225x225

Tsohon Babban Daraktan Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL), Mele Kyari, ya bayyana cewa sammacin kama da Kwamitin Majalisar Dattawa Kan Asusun Jama’a ya bayar a kansa ya ba shi mamaki matuka, yana mai cewa bai ki amsa gayyatar kwamitin ba kamar yadda ake zargi.

Kyari ya bayyana hakan ne a cikin wata wasika da ya aikewa shugaban kwamitin, bayan da majalisar ta bayar da umarnin kama shi sakamakon rashin bayyana a wani zaman bincike da ake gudanarwa kan harkokin kudaden Kamfanin NNPCL.

A cewarsa, tun kafin zaman ya gudana ya sanar da kwamitin cewa yana kasar waje domin samun kulawar lafiya, kuma ya bayyana shirinsa na halartar zaman da zarar ya dawo Najeriya.

“Ina nan a shirye kuma ina da cikakken niyyar mutunta gayyatar kwamitin da bayyana a gabansa da zarar na dawo Najeriya,” in ji Kyari.

Ya musanta zargin cewa ya yi watsi da gayyatar majalisar, yana mai cewa bai samu wata sabuwar sanarwa ko gayyata daga kwamitin ba kafin a bayar da sammacin kama shi.

“Da a ce gayyatar ta same ni, da babu wata-wata zan halarta domin ba ni da abin da nake boyewa,” ya bayyana.

Kyari ya ce halin lafiyarsa a yanzu ba ya ba shi damar komawa gida domin amsa tambayoyin kwamitin, inda ya bukaci a rika tuntubar lauyoyinsa idan akwai wani muhimmin sako yayin da yake ci gaba da jinya.

Tsohon shugaban NNPCL din ya kuma kare aikinsa a lokacin da yake jagorantar kamfanin, yana mai cewa ya taimaka wajen sauya NNPCL daga kamfani mai asara zuwa wanda ke gudanar da harkokinsa bisa tsarin kasuwanci mai anfani.

Ya kara da cewa dukkan mu’amalolin da aka gudanar a lokacin mulkinsa suna da cikakkun bayanai kuma a bude suke ga duk wani bincike na doka.

A halin yanzu dai, Kwamitin Majalisar Dattawa Kan Asusun Jama’a na gudanar da bincike kan wasu bayanan kudade da mu’amalolin NNPCL da ake cewa darajarsu ta haura naira tiriliyan N210.

An bayar da sammacin kama Kyari ne bayan kudirin da Sanata Victor Umeh ya gabatar, tare da goyon bayan Sanata Adams Oshiomhole, bayan ya kasa halartar zaman kwamitin.

Sai dai Kyari ya jaddada cewa yana da niyyar hada kai da binciken majalisar gaba daya, kuma zai bayyana a gaban kwamitin da zarar likitoci sun tabbatar ya samu sauki.

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticleBabu Wanda Ya Fi Ni Cancanta Tsayawa Takarar Shugaban Kasa — Seriake Dickson
Next Article PCN Ta Cafke Mutane Biyar Kan Karya Hatimin Shagunan Magunguna Ba Bisa Ka’ida Ba A Kano

Related Posts

APC Na Tsoron Karfin Accord A Fadin Osun

June 12, 2026

Wasu ‘Yan Najeriya Na Ba ‘Yan Ta’adda Abinci Da Bayanai – Ministan Tsaro

June 12, 2026

Majalisar Wakilai Ta Nada Fred Agbedi Sabon Jagoran ‘Yan Adawa

June 12, 2026

Agbedi Ya Zama Sabon Jagoran ‘Yan Adawa A Majalisar Wakilai, Soro Da Dasuki Sun Samu Mukamai

June 11, 2026
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

Messi Shi Ne Mafi Kyawun Dan Wasa Da Na Taba Gani

June 12, 2026

IPAC Ta Yi Kira Ga Jam’iyyu Su Guji Rikici, Su Tabbatar Da Sahihin Zabe A 2027

June 12, 2026

APC Na Tsoron Karfin Accord A Fadin Osun

June 12, 2026

Wasu ‘Yan Najeriya Na Ba ‘Yan Ta’adda Abinci Da Bayanai – Ministan Tsaro

June 12, 2026

Rashin Tallafin Jama’a Na Kara Haddasa Satar Mutane Da Rashin Tsaro A Najeriya – FIWON

June 12, 2026
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.