Tsohon gwamnan Jihar Bayelsa kuma Sanata mai wakiltar Bayelsa ta Yamma, Seriake Dickson, ya bayyana cewa babu wanda ya fi shi cancanta ya tsaya takarar shugaban kasa a Najeriya, yana mai cewa fitowar Peter Obi a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NDC ba wata alfarma ba ce da ya yi wa jam’iyyar.
Da yake magana a wani shirin talabijin na ARISE PrimeTime, Dickson ya yi watsi da ra’ayoyin da ke cewa Peter Obi ne ya kara wa jam’iyyar NDC karfi da farin jini, yana mai cewa jam’iyyar ce ta ba Obi damar amfani da dandalinta domin neman shugabancin kasa.
“Babu wanda ya fi ni cancanta ya tsaya takarar shugaban kasar Najeriya. Babu ko daya. Ana ambaton wasu sunaye ne saboda sun taba yin takara a baya, amma ni na zabi kada in yi hakan saboda wasu dalilai,” in ji shi.
Sanatan ya kara da cewa bai dace a rika nuna kamar wasu mutane ne ke yi wa jam’iyyar NDC alfarma ba, yana mai jaddada cewa jam’iyyar ce ke yi wa manyan ‘yan siyasa alfarma ta hanyar ba su damar tsayawa takara a karkashinta.
“Kar a nuna kamar wani yana yi wa NDC alfarma. Ba haka ba ne. NDC da shugabanninta ne suke yi wa wasu alfarma ta hanyar ba su damar amfani da dandalin jam’iyyar,” ya bayyana.
Dickson ya kuma gargadi magoya bayan Peter Obi da su guji kalaman da ke cin mutuncin shugabannin jam’iyyar ko kuma tsarin jam’iyyar, yana mai cewa hakan na iya kawo cikas ga hadin kai da zaman lafiya a cikin jam’iyyar.
Ya ce, “Ba za ka ce kana goyon bayan Peter Obi ba sannan a lokaci guda kana cin mutuncina, shugabannin jam’iyya ko kuma jam’iyyar kanta. Hakan ba shi da ma’ana.”
Sai dai duk da kalamansa, Dickson ya sake tabbatar da cewa Peter Obi mutum ne mai muhimmanci a jam’iyyar, inda ya bayyana shi a matsayin daya daga cikin fitattun mambobinta da aka ba tikitin takarar shugaban kasa.
“Peter Obi mamba ne da muke daraja a jam’iyyarmu, kuma mun ba shi tikitin takarar shugaban kasa. Wannan ma abu ne mai muhimmanci,” in ji shi.
Dickson ya kuma bayyana cewa jam’iyyar NDC ta janyo hankalin manyan ‘yan siyasa daga sassa daban-daban na kasar nan tun kafin da kuma bayan fitowar Peter Obi a matsayin dan takararta na shugaban kasa.
