Kusan mutane 20, galibi manoma masu kiwon kifi da masu sare itace, sun rasa rayukansu yayin da wasu da dama suka jikkata bayan wani bam da ake zargin ‘yan ta’addan Boko Haram ne suka dasa ya fashe a bayan garin Gwoza, Jihar Borno.
Majiyoyi daga yankin sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:00 na safe a ranar Alhamis a ƙauyen Hambagda, wanda aka sake tsugunar da mutane, kuma yake ‘yan kilomita kaɗan daga garin Gwoza.
A cewar wani mamba na Civilian JTF, yawancin wadanda suka mutu sun fita ne zuwa daji domin neman itacen girki da kuma shirin noma kafin lokacin damina.
“Rana ce mai alhini gare mu a Gwoza. Mun rasa kusan masu sare itace 20, sannan wasu da dama sun jikkata. ‘Yan ta’adda sun dasa bama-bamai (IEDs) a kan hanya, bayan fashewar kuma suka buɗe wuta kan fararen hula marasa laifi,” in ji majiyar CJTF.
Wata majiya kuma ta bayyana cewa manoma da masu tattara itace ne aka kai wa harin yayin da suke gudanar da ayyukansu na yau da kullum a daji.
Wani mazaunin yankin ya tabbatar cewa an gano aƙalla gawarwaki 18 zuwa yanzu a ƙauyukan da ke kusa da Gwoza, yana mai gargadin cewa adadin wadanda suka mutu na iya ƙaruwa saboda akwai wasu da ba a san inda suke ba.
Mazauna yankin sun kuma ce maharan na tafiya suna kai hare-hare a sassa daban-daban na yankin, lamarin da ya ƙara haifar da fargaba ga manoma yayin da lokacin shuka ke gabatowa.
An danganta harin da ake zargin ya yi sanadin wannan mummunan lamari da ayyukan Boko Haram, wacce ke ci gaba da kai hare-hare da kuma dasa bama-bamai a wasu sassan Arewacin Borno.
