Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta mika wani wanda ake zargi da laifukan kisan kai da safarar miyagun kwayoyi, Matthew Chukwuemeka Adebiyi, zuwa kasar Birtaniya domin gurfanar da shi a gaban kotu.
Rundunar ta ce an gudanar da aikin mika shi ne ta hannun ofishin INTERPOL na Najeriya da ke Abuja, bayan bukatar da hukumomin Birtaniya suka aike tun a watan Satumba 2024 domin a gano shi, a kama shi tare da mika shi.
A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, Anthony Placide, ya fitar a ranar Alhamis, ya ce ana zargin Adebiyi da kisan wani mai suna Joshua Boadu a ranar 18 ga Yuni, 2018, lamarin da ya sa ya tsere zuwa Najeriya domin gujewa kama shi.
Haka kuma, ana zarginsa da hannu wajen safarar crack cocaine, wani nau’in muggan kwayoyi na Class-A, tsakanin Oktoba 2017 zuwa Maris 2018 a Birtaniya.
Placide ya ce an kama wanda ake zargin a ranar 23 ga Janairu, 2025 ta hannun jami’an INTERPOL NCB Abuja, bayan haka aka fara shari’ar neman mika shi a Babbar Kotun Tarayya da ke Lagos, a shari’ar mai lamba FHC/L/CS/416/2025.
Ya kara da cewa a ranar 16 ga Fabrairu, 2026, kotu ta amince da bukatar mika shi bisa doka.
Sanarwar ta ce a ranar 14 ga Afrilu, 2026, an mika shi a hukumance ga jami’an tsaro na Birtaniya a filin jirgin sama na Murtala Muhammed da ke Lagos domin ci gaba da shari’a.
Sufeton Janar na ‘Yan Sanda, Olatunji Rilwan Disu, ya jaddada aniyar rundunar wajen hadin gwiwa da kasashen waje domin yaki da laifuka.
Ya kara da cewa Najeriya ba za ta zama mafakar masu aikata laifi ba.
