Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta bayyana cewa ba kasa da masu zabe 673,446 ne za su kada kuri’a a ranar 20 ga Yuni domin zaben sabon sanata na mazabar Ondo Kudu.
Zaben na zuwa ne bayan gurbin kujerar ya samu vacanci sakamakon nada tsohon dan majalisa, Jimoh Ibrahim, a matsayin Wakilin Dindindin na Najeriya a Majalisar Dinkin Duniya.
Kwamishinan Zabe na Jihar Ondo, Dakta Mutiu Olaleke Agboke, ya bayyana hakan yayin taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Okitipupa, hedikwatar mazabar.
Ya ce Majalisar Dattawa ta ayyana kujerar babu kowa a ranar 28 ga Afrilu, 2026, sannan ta umarci INEC da ta gudanar da zaben cike gurbi bisa tanadin kundin tsarin mulki.
Agboke ya ce masu zaben za su kada kuri’a a rumfunan zabe 1,354 da kuma yankunan rajista 66 da ke cikin kananan hukumomi shida na mazabar, wadanda suka hada da Ile-Oluji/Oke-Igbo, Odigbo, Irele, Ilaje, Ese-Odo da Okitipupa.
Ya bayyana cewa an kammala tantance rajistar masu zabe tare da tsaftace ta, yana mai cewa ci gaba da rajistar masu zabe ba zai shafi jerin da za a yi amfani da shi a zaben ba.
Haka kuma an raba kayan zabe marasa muhimmanci, yayin da za a mika na muhimmanci a gaban jam’iyyun siyasa da jami’an tsaro domin tabbatar da gaskiya da tsari.
Agboke ya ce an gwada na’urorin BVAS 1,359 tare da tabbatar da ingancinsu, sannan an ajiye karin 264 domin amfani idan bukata ta taso.
Ya tabbatar da cewa INEC ta shirya tsaf domin gudanar da zaben, yana mai cewa kuri’un da jama’a suka kada ne kawai za su yanke hukuncin wanda zai lashe zaben.
Ya kuma bukaci ‘yan siyasa da masu kada kuri’a da su kiyaye zaman lafiya kafin, lokacin da kuma bayan zaben, yayin da jam’iyyun APC, APM, APP da Boot Party za su fafata.
