Gabanin zaben fidda gwani na shugaban kasa na shekarar 2027, jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta tantance tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, da tsohon Manajan Daraktan FSB International Bank, Mohammed Hayatu-Deen.
An gudanar da tantancewar ne a ranar Laraba a otal din Transcorp Hilton da ke Abuja karkashin wani kwamiti da tsohon gwamnan jihar Cross River, Liyel Imoke, ke jagoranta, yayin da Cyril Maduabum ke matsayin sakatare.
Hayatu-Deen ya isa wajen tantancewar da misalin karfe 10:50 na safe, inda ya shafe kusan awa guda yana amsa tambayoyi daga kwamitin. Shi kuma Atiku ya isa da misalin karfe 12:06 na rana.
Da yake magana da manema labarai bayan tantancewar, Hayatu-Deen ya bayyana gamsuwarsa da yadda aka gudanar da tsarin, yana mai cewa a shirye yake domin duk hanyar da jam’iyyar za ta bi wajen zakulo dan takara.
“Na shafe kusan awa guda a cikin dakin tantancewa kuma komai ya tafi lafiya. Yanzu muna wani muhimmin mataki na siyasa inda za a iya zabar dan takara ta hanyar maslaha ko kuma zaben kai tsaye,” in ji shi.
Ya kara da cewa idan har ya samu tikitin jam’iyyar, zai gudanar da yakin neman zabe mai cike da tsari da mayar da hankali wajen magance matsalolin tsaro, tsadar rayuwa, rashin aikin yi, matsalar lantarki da tabarbarewar ilimi da lafiya.
Hayatu-Deen ya kuma ce ya dade yana shirye domin wannan takara, yana mai cewa shiga irin wannan fafatawa na bukatar cikakken shiri da sadaukarwa.
Bayan Hayatu-Deen ya bar wajen, Atiku Abubakar ya shiga dakin tantancewar domin ganawa da kwamitin.
Sai dai bayan fitowarsa, Atiku bai yi dogon bayani ga manema labarai ba, illa cewa “tantancewar ta tafi lafiya.”
Atiku, wanda ya taba neman shugabancin kasa sau da dama tun daga shekarar 1993, na daga cikin fitattun jagororin adawa a Najeriya. Shigarsa takarar ADC na zuwa ne yayin da ake ci gaba da tattaunawar hadaka tsakanin jam’iyyun adawa gabanin zaben 2027.
A daya bangaren kuma, Mohammed Hayatu-Deen ana kallonsa a matsayin daya daga cikin masu kishin sauye-sauyen tattalin arziki da gyaran hukumomi a cikin jam’iyyar.
Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, ana jiran tsohon gwamnan jihar Rivers kuma tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, domin nasa tantancewar.
Jam’iyyar ADC na sa ran kammala tantancewar kafin yanke hukuncin ko za ta bi hanyar maslaha ko kuma zaben kai tsaye wajen fitar da dan takararta na shugaban kasa a 2027.
