Tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, ya bukaci masu neman takara a jihar da su rungumi hadin kai, hakuri da kuma gina shugabanci mai tasiri yayin da harkokin siyasa ke kara daukar zafi gabanin zabubbuka masu zuwa.
Bello ya yi wannan kiran ne yayin da ya karɓi ‘yan Majalisar Dokokin Jihar Kogi, kamar yadda wata sanarwa daga ofishin yada labaransa ta bayyana a Lokoja ranar Litinin.
Taron na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun karuwar tattaunawa da sauye-sauyen siyasa a jihar bayan rantsar da Gwamna Ahmed Usman Ododo, wanda ya gaji Bello kuma abokin siyasarsa ne.
Bello, wanda ya mulki Kogi daga 2016 zuwa 2024, har yanzu yana da tasiri sosai a tsarin siyasar jihar karkashin jam’iyyar APC.
A cewar kakakin sa, Michael Ohiare, Bello ya taya dukkan masu neman takara murna bisa karɓar fom ɗin shiga takara, inda ya tunatar da su cewa siyasa abu ne na wucin gadi.
“Ya ce siyasa abu ne mai wucewa, kuma kowane shugaba zai bar matsayinsa wata rana,” in ji sanarwar.
Bello ya jaddada cewa abin da ya fi muhimmanci ba mukami ba ne, illa abin da mutum ya bari na kyakkyawan tarihi da tasiri ga al’umma.
Ya kuma bukaci ‘yan takara da su mutunta wadanda suka janye domin ba su dama, yana mai cewa irin wannan sadaukarwa ya kamata a daraja ta.
Bugu da kari, ya gargadi cewa babu wanda ya kamata a tilasta masa biyan kudi domin samun goyon baya, inda ya ce duk wanda aka nema da kudi ya kamata a mayar masa da shi.
Tsohon gwamnan ya kuma shawarci ‘yan takara da su koma yankunansu domin yin sulhu da hada kan jama’a, yana mai jaddada muhimmancin hadin kai da shiga lamarin al’umma kai tsaye.
Ya nuna kwarin gwiwa kan nasarar su a zabe, yana mai cewa dole ne a hada nasara da hidima ga jama’a domin dorewa.
A nasa bangaren, Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kogi, Rt. Hon. Umar Aliyu, ya yabawa Bello kan gina tubalin hadin kai a majalisar, wanda ya ce ya ci gaba a karkashin Gwamna Ododo.
Ya kuma tabbatar da biyayyarsu ga Bello da gwamnatin yanzu, tare da alkawarin ci gaba da goyon bayan manufofin gwamnatin jihar.
Rahotanni sun kuma nuna cewa yawan kujerun majalisar dokokin jihar ya karu daga 25 zuwa 36 gabanin zabubbuka masu zuwa sakamakon sabon tsarin wakilci.
