Faston ya bayyana hakan ne a wani bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta, inda ya yi ikirarin cewa burin Adelabu na siyasa na iya fuskantar cikas koda kuwa jam’iyyar APC ta tsayar da shi a matsayin ɗan takara.
Ayodele ya ce “mabudin nasara” na Adelabu yana hannunsa, kuma ya bukace shi da ya zo domin karɓar jagorancinsa.
Ya ce:
“Ya ɗana Bayo Adelabu, kai ɗana ne, ina sonka, amma idan ka rasa hanya, abin da kake bukata domin zama gwamna yana hannuna. Zo ka karɓa. Ka gwada, ko APC ta tsayar da kai, idan ba ka karɓa ba, za ka yi rashin nasara.”
Faston ya ƙara da wasu kalamai masu ƙarfi game da rawar da yake ikirarin takawa a siyasar Adelabu.
Ya ce:
“Bari in yi alfahari a matsayina na limami, idan ka isa can, babu Allah kuma. Abin da kake bukata domin zama gwamna yana hannuna. Na faɗa, Allah ne ya gaya min. Duk wanda ya kira shi da wani suna, ni kawai ina ƙalubalantar ka cewa domin zama gwamna, abin da kake bukata yana cikin aljihuna. Idan ka ci zaɓe, babu Allah.”
Wannan magana ta jawo martani da muhawara mai zafi a kafafen sada zumunta, inda mutane da dama ke sukar irin wannan ikirari da ke danganta ikon Allah da nasarar siyasa.
A gefe guda kuma, rahotanni sun bayyana cewa Bayo Adelabu ya yi murabus daga muƙaminsa a gwamnatin Shugaba Bola Tinubu domin tsunduma takarar gwamnan Oyo a zaɓen 2027.
