Shahararren mai tallafa wa harkokin kwallon kwando a Najeriya kuma wanda ya kafa shirin Mark D’Ball, Igoche Mark, ya shiga jimami bayan rasuwar mahaifiyarsa, Misis Oyiba Veronica Mark.
A cikin wata sanarwa da iyalanta suka fitar, an bayyana cewa Misis Oyiba Veronica Mark ta rasu cikin kwanciyar hankali a ranar Litinin, 29 ga Yuni, 2026.
Iyalan mamaciyar sun bayyana alhininsu tare da mika komai ga nufin Allah Madaukakin Sarki.
Sanarwar ta ce, “Cikin matukar bakin ciki amma da cikakkiyar mika wuya ga nufin Allah, iyalan Misis Oyiba Veronica Mark na sanar da rasuwar mahaifiyarmu, kakarmu, ‘yar uwarmu kuma abokiyarmu.”
Sun bayyana marigayiyar a matsayin mace mai cike da imani, kauna, juriya da tausayi, wadda ta sadaukar da rayuwarta wajen kula da iyali da al’umma.
A cewar iyalan, kyawawan halayenta, hikimarta da jajircewarta wajen hidimtawa jama’a sun bar abin koyi da za a ci gaba da tunawa da shi.
Sun ce duk da cewa rasuwarta ta bar babban gibi a zukatansu, suna samun kwanciyar hankali ta hanyar kyawawan abubuwan tunawa da ta bari da kuma fatan tana cikin hutu na har abada.
Igoche Mark na daga cikin fitattun masu bunkasa wasan kwallon kwando a Najeriya, kuma an fi saninsa da kafa shirin Mark D’Ball, wanda ya taimaka wajen gano da bunkasa hazikan matasa masu baiwar wasan kwallon kwando a sassa daban-daban na kasar.
Iyalan sun ce za su sanar da jadawalin jana’izar marigayiyar nan gaba, tare da gode wa dangi, abokai da masu yi musu fatan alheri bisa addu’o’i da goyon bayan da suke ba su a wannan lokaci na jimami.
