Kungiyar masu kula da gidajen marayu ta Najeriya (ASOHON) reshen Jihar Oyo tare da hadin gwiwar Child Protection Network (CPN), sun bukaci a gaggauta sakin daliban makaranta da shugabar makarantarsu da aka sace a Ibadan a watan da ya gabata.
Da take jawabi a wani taron manema labarai da aka gudanar a Ibadan, jami’ar hulda da jama’a ta ASOHON, Hajiya Abimbola Abraham-Adegboyega, ta ce masu rajin kare hakkin yara, shugabannin al’umma da sauran masu ruwa da tsaki sun taru ne domin nuna damuwa kan lamarin tare da kira ga hukumomi su dauki matakin gaggawa.
Ta bayyana cewa ya kamata yara su kasance a makarantu da gidajensu, ba a hannun masu garkuwa da mutane ba.
“Wannan sacewar ta shafi iyalai da al’umma baki daya, kuma ta sake jawo hankali kan batun tsaron yara. Yaranmu da dukkan ‘yan Najeriya sun cancanci zaman lafiya da makoma mai kyau,” in ji ta.
Abraham-Adegboyega ta ce kungiyar na matukar damuwa da yadda har yanzu yaran da shugabar makarantar ke ci gaba da zama a hannun masu garkuwa da su, tana mai gargadin cewa hakan na iya kara musu raunin zuciya da damuwa.
Ta yi kira ga jami’an tsaro da su kara kaimi tare da amfani da dukkan hanyoyin da suka dace domin ceto wadanda aka sace.
“Mun bukaci jami’an tsaro su yi amfani da dukkan kayan aiki da dabarun da suke da su domin ceto yaran cikin gaggawa. Suna bukatar kariya, kulawar lafiya da kuma komawa ga iyalansu cikin koshin lafiya,” ta ce.
Ta kuma bukaci gwamnatoci a dukkan matakai su kara daukar matakan kare makarantu ta hanyar inganta tattara bayanan sirri da tsaro a cibiyoyin ilimi.
Haka kuma, ta roki jama’a da su taimaka wa jami’an tsaro ta hanyar bayar da duk wata sahihiyar bayanai da za ta taimaka wajen kubutar da wadanda aka sace.
“Idan kana da wani bayani, ka sanar da hukumomin da abin ya shafa. Bayanin da aka bayar a kan lokaci na iya ceton rayuka,” in ji ta.
Ta kuma yi kira ga masu garkuwa da yaran da su sake su ba tare da wani sharadi ba, tana mai cewa bai kamata yara su zama wadanda za su sha wahala sakamakon wata matsala ko rikici ba.
A cewarta, ASOHON da CPN a shirye suke su taimaka wajen kula da yaran bayan an sake su, ta hanyar ba su shawarwari, kulawar lafiya da taimakon komawa rayuwa ta yau da kullum.
“Babu wani yaro da ya kamata ya fuskanci murmurewa shi kadai,” ta kara da cewa.
Kungiyoyin sun sake jaddada aniyarsu ta ci gaba da fafutukar kare hakkin yara da tabbatar da cewa an dawo da dukkan wadanda aka sace gida lafiya.
