Tsohon gwamnan jihar Kano kuma Sanatan Kano ta Tsakiya, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana kwarin gwiwar samun tikitin mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) gabanin babban zaben shekarar 2027.
Kwankwaso ya ce idan hakan ta tabbata, zai zama babban tarihi ga jihar Kano tare da kara kusantar burinta na samar da shugaban kasa daga jihar a nan gaba.
Ya bayyana hakan ne yayin wata hira da ya yi da Premier Radio, inda ya ce zaben 2027 zai kasance lokaci mai muhimmanci ga Kano da Najeriya idan har sunansa ya bayyana a takardar zabe a matsayin mataimakin shugaban kasa.
“Da yardar Allah, zabe mai zuwa zai kasance daban da duk abin da aka taba gani a jiharmu da kasa baki daya, musamman idan na samu tikitin kuma sunana ya kasance cikin masu takara,” in ji Kwankwaso.
Tsohon gwamnan ya nuna takaicinsa kan yadda jihar Kano ba ta taba samar da mataimakin shugaban kasa ba tun daga Jamhuriya ta Farko duk da irin tasirin siyasar jihar a Najeriya.
“Tun daga Jamhuriya ta Farko, duk da irin gwagwarmaya da hikimar siyasar da muke da ita, Kano ba ta taba samar da mataimakin shugaban kasa ba. Wannan abin takaici ne sosai, amma da yardar Allah za a gyara hakan,” ya bayyana.
Kwankwaso ya kara da cewa samun wannan mukami zai bude kofar da Kano za ta iya samar da shugaban kasa a nan gaba.
Ya kuma yi kira ga shugabannin siyasa a Arewa musamman yankin Arewa maso Yamma da su yi taka-tsantsan wajen yanke hukunci kafin zaben 2027 domin kauce wa nadamar siyasa.
“Akwai mutanen kudu da suka fahimci abin da ke faruwa kuma suna shiga jam’iyyarmu. Arewa musamman Arewa maso Yamma dole ta yi hankali wajen yanke hukunci domin kada a yi nadamar siyasa daga baya,” in ji shi.
Kwankwaso dai ya koma jam’iyyar NDC ne bayan ficewarsa daga ADC, inda ya kasance cikin hadakar jam’iyyun adawa a baya.
