Wasu daliban Jami’ar Cross River sun gudanar da zanga-zanga a Calabar ranar Litinin, inda suka dora alhakin mutuwar dalibai uku kan rashin ingantattun kayan aiki da cibiyoyin kula da lafiya a Babban Asibitin Calabar.
Lamarin ya biyo bayan wani mummunan hatsarin mota da ya faru ranar Juma’a a hanyar Calabar zuwa Itu, inda motar da ke dauke da daliban ta yi karo da wata babbar mota.
Rahotanni sun nuna cewa direban motar da dalibai uku sun rasa rayukansu sakamakon munanan raunukan da suka samu.
Daliban na dawowa ne daga wasan kwallon kafa da suka je yi a Jami’ar Uyo da ke Jihar Akwa Ibom lokacin da hatsarin ya afku.
A yayin zanga-zangar, daliban sun fito da alluna masu dauke da rubuce-rubuce da ke zargin rashin kayan aiki da ingantacciyar kulawa a asibitin da suka ce ya taimaka wajen rasa rayukan abokan karatunsu.
Zanga-zangar ta rikide zuwa tashin hankali lokacin da wasu daga cikin masu zanga-zangar suka kai hari ga ma’aikatan asibitin tare da lalata wasu kayayyaki da gine-gine.
Sai dai jami’an ‘yan sanda sun isa wurin tare da tarwatsa su lokacin da suka nufi ofishin gwamnan jihar domin ci gaba da zanga-zangar.
Lamarin ya haifar da damuwa a jihar, yayin da ake kira ga hukumomi su binciki musabbabin mutuwar daliban da kuma inganta tsarin kula da lafiya domin kauce wa irin wannan asara a gaba.
