Ofishin Jakadancin Amurka a Najeriya ya bayyana cewa dangantakar da ke tsakanin Najeriya da Amurka ba ta tsaya ga hulɗar gwamnati da gwamnati kaɗai ba, tana kuma haɗa da alaƙa mai ƙarfi tsakanin al’umma, cibiyoyi da kuma ɓangaren kasuwanci na ƙasashen biyu.
Jakadancin ya ce waɗannan haɗin gwiwa na ci gaba da taimakawa wajen ƙarfafa zaman lafiya, faɗaɗa damar tattalin arziki, da kuma inganta rayuwar al’umma a ƙasashen biyu.
Wannan sabon tabbatarwa na zuwa ne a daidai lokacin da ƙasashen biyu ke ci gaba da tattaunawa kan muhimman batutuwa kamar yaki da ta’addanci, sauƙaƙe kasuwanci, shirye-shiryen musayar ilimi, da kuma harkokin kiwon lafiya.
Jami’ai sun bayyana cewa dangantakar da ta daɗe tana ci gaba da kasancewa muhimmin ginshiƙi a hulɗar Najeriya da Amurka a Afirka da ma sauran sassan duniya.
