Tsohon Gwamnan Jihar Ogun kuma Sanatan Ogun East, Otunba Gbenga Daniel, ya bayyana cewa an hana shi shiga taron masu ruwa da tsaki na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) da ke gudana a Adeola Odutola Hall, Ijebu Ode, a ranar Litinin.
Daniel ya bayyana hakan ne a cikin wani bidiyo mai tsawon kusan minti ɗaya da ya bazu a kafafen sada zumunta.
A cikin bidiyon, an ga tsohon gwamnan yana magana daga cikin motar yakin neman zabensa mai launin fari wadda ke dauke da tambarin OGD/PBAT Movement.
Ya ce: “Mun zo taron kwamitin APC na Ogun East, amma abin mamaki an hana mu shiga. An ce ba za mu iya shiga ba. Amma bari a sani cewa duk abin da aka yi a nan yau ba shi da inganci.”
Takardar gayyatar taron gaggawa na masu ruwa da tsaki da shugabancin jam’iyyar APC a Ijebu Ode ya fitar, ta kunshi gayyatar mataimakan gwamna, tsofaffi da na yanzu na shugabannin ƙananan hukumomi, kansiloli, da kuma tsofaffi da na yanzu ‘yan majalisun jiha da na tarayya, da sauransu da ake sa ran hala the torta.
