Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    KOTU TA SAMU MACE DA LAIFIN YUNKURIN KASHE ƳAR SHEKARA 9 BAYAN TA YAUDARE TA ZUWA DAJI

    June 26, 2026

    KOTU TA KI SAKIN SOWORE, TA DAGE YANKE HUKUNCI ZUWA 30 GA YUNI

    June 24, 2026

    Sarkin Ilorin Ya Taya Musulmi Murnar Sabuwar Shekarar Hijira, Ya Yi Kiran Hadin Kai

    June 16, 2026

    Ranar Dimokuradiyya: SDP Ta Bukaci Shugabanni Su Yi Mulki Da Gaskiya Da Kishin Kasa

    June 12, 2026

    📰 Labarin Yanar Gizo (Hausa Version): Kaduna Pilgrims Board Ya Tabbatar An Yi Hadaya Ga Duk Masu Biyan Kuɗi

    June 9, 2026

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Zafin Rana Mai Tsanani Ya Ɓarke a Turai: Matsalar Heat Dome

    June 30, 2025

    July 3, 2026

    Majalisar Iran Ta Bukaci Jama’a Su Halarci Jana’izar Jagoran Addini Domin Nuna Hadin Kai

    July 2, 2026

    Kalaman Remi Tinubu kan sana’ar ƙosai da gasasshen masara sun jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta

    June 26, 2026

    Gwamnatin Tarayya ta yabawa jakadan Najeriya bayan sakin ‘yan Najeriya da aka tsare a Côte d’Ivoire

    June 26, 2026
  • Asrah 24 TV
  • Education

    NELFUND Na Binciken Makarantu 34 Kan Rashin Mayar Wa Dalibai Kudin Makaranta

    July 6, 2026

    ‘Yar Najeriya Ta Kammala Karatun Likitanci a Rasha da Makin 4.90 CGPA

    July 6, 2026

    Portable Ya Ce Zai Koma Makaranta Domin Kammala Karatunsa

    July 6, 2026

    Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Gudanar da Gwajin Kwarewar Dalibai Duk Bayan Shekaru Uku – Alausa

    July 3, 2026

    Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Sauya Kakin NYSC Da Tufafin Adire

    July 2, 2026
  • Health

    Majalisar Dattawa Ta Gabatar Da Kudirin Kirkirar Tsarin Lafiya Na Zamani Zuwa Karatu Na Biyu

    July 8, 2026

    “Ba Abu Ne Mai Sauƙi Ba” – Wata Uwar da Ta Yi Surrogacy Ta Bayyana Kalubalen da Ta Fuskanta

    July 7, 2026

    Jinyar Mace Ta Karya Al’adar Addinin Buddha Domin Ceto Rayukan Sufaye Bayan Mummunan Hatsari

    July 3, 2026

    Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Karfafa Hadin Gwiwa Da Cibiyoyin Bincike Domin Dakile Barkewar Cututtuka

    July 2, 2026

    TETFund ta ƙalubalanci masana kimiyya su gaggauta samar da rigakafin cutar Lassa Fever na farko a Najeriya

    June 30, 2026
  • Podcast
  • Politics

    Tinubu Ya Aika Sunan Lamido Yuguda Domin Shugabancin AMCON

    July 8, 2026

    Majalisar Dattawa Ta Amince Da Nada Dr. Zainab Marwa A Hukumar NDDC

    July 8, 2026

    Rigima Ta Barke A Majalisar Wakilai Kan Bukatar A Gayyaci Tinubu

    July 8, 2026

    Mai Yiwuwa Ba Zan Kai Ga Tsayawa Takarar 2027 Ba cewar Peter Obi

    July 8, 2026

    An Binciki PFIPC: Adeyemi Ya Sha Alwashin Bai Wa ICPC Hadin Kai

    July 8, 2026
  • Sports

    Messi Ya Kafa Sabon Tarihi A Gasar Kofin Duniya Ta FIFA

    July 8, 2026

    Masar Ta Bukaci FIFA Ta Hukunta Alkalan Wasanta Da Argentina

    July 8, 2026

    Yusuf Alli Ya Bukaci ‘Yan Wasan Najeriya Su Zama Masu Ladabi Gabanin Wasannin Commonwealth 2026

    July 6, 2026

    Kwara United Ta Sanya Ranar Komawa Sansani Gabanin Sabon Kakarar NPFL

    July 2, 2026

    Coco Gauff Ta Bayyana Yadda Gwajin Hana Amfani da Kwayoyin Kara Kuzari Ya Taba Sanya Ta Yin Kuka

    July 2, 2026
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home » Najeriya Na Iya Daukar Mataki Kan Kamfanonin Afirka Ta Kudu – Bianca Ojukwu
Agriculture

Najeriya Na Iya Daukar Mataki Kan Kamfanonin Afirka Ta Kudu – Bianca Ojukwu

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaJune 18, 20263 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp
Bianca Ojukwu 1024x1024

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa tana duba yiwuwar daukar wasu matakai kan kamfanonin Afirka ta Kudu da ke gudanar da kasuwanci a Najeriya idan hare-haren kyamar baki da ake yi wa ‘yan Najeriya a Afirka ta Kudu suka ci gaba.

 

Ministar Harkokin Wajen Najeriya, Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu, ta bayyana hakan yayin da take magana kan yadda ake ci gaba da muzgunawa da kuma kai hare-hare kan ‘yan Najeriya da ke zaune a kasar Afirka ta Kudu.

 

Ta ce duk da cewa Najeriya ta dade tana bin hanyoyin diflomasiyya da tattaunawa wajen warware matsalar, gwamnati na iya sake nazarin wasu zabuka idan har ba a kawo karshen hare-haren ba.

 

A cewarta, akwai sama da kamfanonin Afirka ta Kudu 120 da ke gudanar da harkokinsu a Najeriya, kuma babu wanda ke muzgunawa ma’aikatansu ko hana su gudanar da kasuwanci.

 

“Ba wanda ke tambayar ma’aikatan kamfanonin Afirka ta Kudu a Najeriya ko su ‘yan Afirka ta Kudu ne ko ‘yan Najeriya. Ba wanda ke kwace musu shaguna ko kasuwancinsu. Amma wannan shi ne abin da ke faruwa ga ‘yan Najeriya a Afirka ta Kudu,” in ji ta.

 

Ta ambaci manyan kamfanonin Afirka ta Kudu da ke aiki a Najeriya kamar MTN, MultiChoice, Stanbic da Protea, tana mai cewa gwamnati za ta iya duba hanyoyin da suka dace domin kare muradun ‘yan kasarta.

 

Sai dai ministar ta jaddada cewa duk wani mataki da za a dauka dole ne ya bi kundin tsarin mulkin kasa da kuma hanyoyin doka da majalisa ta tanada.

 

Ta bayyana cewa a halin yanzu gwamnatin Najeriya na ci gaba da tattaunawa da hukumomin Afirka ta Kudu ta hanyar diflomasiyya, yayin da Majalisar Dokoki za ta taka muhimmiyar rawa idan har aka bukaci daukar wasu matakai na gaba.

 

Bianca Odumegwu-Ojukwu ta kuma bayyana cewa hukumomin Afirka ta Kudu sun yi watsi da yarjejeniyar fahimtar juna da suka kulla da Najeriya a watan Oktoban 2025 domin samar da tsarin gargadin gaggawa da kariya ga rayuka da dukiyoyin ‘yan kasashen biyu yayin rikice-rikice.

 

Ta ce abin damuwa ne yadda wasu ‘yan Najeriya da suka shafe shekaru suna rayuwa a Afirka ta Kudu, ciki har da wadanda suka auri ‘yan kasar kuma suka haifi yara a can, ke fuskantar matsin lambar barin kasar tare da iyalansu.

 

Tun a watan Mayun bana, Sanatan Edo ta Arewa, Adams Oshiomhole, ya bukaci a soke lasisin wasu kamfanonin Afirka ta Kudu da ke aiki a Najeriya, ciki har da MTN da MultiChoice, sakamakon sabbin hare-haren kyamar baki da ake yi wa ‘yan Najeriya a kasar.

 

Lamarin na ci gaba da janyo muhawara, yayin da ake kira ga gwamnatocin kasashen biyu da su nemo mafita cikin gaggawa domin kare rayuka, dukiyoyi da kuma kyakkyawar alakar diflomasiyya tsakanin Najeriya da Afirka ta Kudu

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticleKamfani Ya Goyi Bayan Raba Taraktoci Da Tinubu Ke Yi, Ya Nemi Horar Da Manoma Domin Samun Cikakken Amfani
Next Article Bincike Ya Nuna Ta’addanci Da Rikicin Manoma Da Makiyaya Na Kara Talauta Al’ummar Arewacin Najeriya

Related Posts

ELRA Da NADF Sun Kulla Yarjejeniya Don Fadada Samun Injinan Noma Ga Manoma

June 10, 2026

FG ta fara tattaunawa da kamfani domin inganta noman zamani a fadin Najeriya

April 24, 2026

NBS:An Samu Raguwar Hauhawar Farashin Kayayyaki a Junairu 2025

February 18, 2025
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

Ministan Tsaro Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Harbe ’Yan Ta’adda Ba Tare Da Jira Umarni Ba

July 8, 2026

Tinubu Ya Aika Sunan Lamido Yuguda Domin Shugabancin AMCON

July 8, 2026

Messi Ya Kafa Sabon Tarihi A Gasar Kofin Duniya Ta FIFA

July 8, 2026

Sabon Mamban Kwamitin TETFund Ya Yi Alƙawarin Yin Aiki Cikin Gaskiya

July 8, 2026

Majalisar Dattawa Ta Gabatar Da Kudirin Kirkirar Tsarin Lafiya Na Zamani Zuwa Karatu Na Biyu

July 8, 2026
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.