Asusun Ba da Lamunin Karatu na Gwamnatin Tarayya (NELFUND) ya fara binciken manyan makarantu 34 bisa zargin kin mayar wa wasu dalibai kudin makaranta da suka biya bayan an sake biyan makarantar kudin ta hanyar shirin lamunin karatu na gwamnati.
Manajan Daraktan NELFUND, Akintunde Sawyerr, ne ya bayyana hakan yayin wata hira da ARISE NEWS, inda ya ce binciken ya biyo bayan koke-koke da dama daga daliban da abin ya shafa.
Ya ce wasu dalibai sun biya kudin makaranta da kansu kafin shirin lamunin dalibai ya fara aiki, daga baya kuma NELFUND ta sake biyan kudin ga makarantunsu, lamarin da ya haifar da biyan kudi sau biyu.
Sawyerr ya bayyana cewa alhakin mayar da kudin yana kan makarantun da suka karbi kudin sau biyu, ba NELFUND ba.
Ya ce dalibai da dama sun karbo bashi daga iyayensu ko wasu mutane domin biyan kudin makaranta, don haka suna bukatar a mayar musu da kudinsu cikin gaggawa.
A cewarsa, wasu makarantu sun mayar da kudin cikin lokaci, yayin da wasu kuma suka gaza yin hakan.
Shugaban NELFUND ya kara da cewa hukumar na inganta tsarin biyan kudin makaranta ta hanyar amfani da fasahar zamani, inda dalibai za su iya amincewa da biyan kudin ta amfani da wata hanyar lantarki a wayoyinsu.
Ya bayyana cewa NELFUND ta zabi biyan kudin makaranta kai tsaye ga cibiyoyin ilimi domin kauce wa yiwuwar karkatar da kudin idan aka bai wa dalibai kai tsaye.
Sai dai ya bayyana cewa hukumar ba ta da ikon kama ko gurfanar da makarantun da suka ki mayar da kudin, saboda haka tana aiki tare da Hukumar EFCC, ICPC, kungiyar dalibai ta kasa (NANS) da masu bincike na cikin gida domin gudanar da bincike.
Sawyerr ya kuma ce NELFUND ta ki biyan kudin makarantu da suka kara kudin makaranta fiye da yadda ya dace bayan fara shirin lamunin dalibai.
Ya tabbatar da cewa hukumar za ta ci gaba da bincike tare da daukar matakan da suka dace domin kare hakkokin daliban Najeriya.
