Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) a zaben 2027, Peter Obi, ya bayyana cewa akwai yiwuwar ma ba zai kai ga tsayawa takarar shugaban kasa ba, yana mai zargin cewa ana hana shi gudanar da harkokinsa tare da matsa wa ‘yan adawa lamba.
Obi ya bayyana hakan ne a wata hira da shirin With Chude, inda ya ce duk abin da yake kokarin yi gwamnati na kawo masa cikas.
Ya ce, “Ba wai kawai ba zan zama dan takara ba, akwai yiwuwar ma ba zan kasance a raye ba. Duk abin da nake yi ana kokarin hana ni.”
Tsohon gwamnan Jihar Anambra ya ce ba ya zargin kowa kai tsaye, amma yana ganin alamun cewa ana hana shi gudanar da ayyukansa cikin ‘yanci.
A cewarsa, ba shi kadai ake yi wa hakan ba, har da sauran fitattun ‘yan adawa.
Obi ya bayar da misalin wani abin da ya ce ya faru da shi a filin jirgin sama, inda aka kulle motarsa duk da cewa akwai wasu motocin da aka bari ba tare da wata matsala ba.
Ya kuma yi ikirarin cewa wasu mutane na kauce wa gaishe shi a bainar jama’a saboda tsoron kada a dauke su a matsayin masu goyon bayansa. Haka kuma, ya ce wasu ma kan bukace shi da kada ya halarci bukukuwan iyalansu saboda irin wannan tsoro.
Sai dai Peter Obi bai gabatar da wata hujja da ke tabbatar da zarge-zargen nasa ba, yayin da har zuwa lokacin wallafa wannan rahoto, Gwamnatin Tarayya ba ta fitar da wata sanarwa domin mayar da martani kan kalaman nasa ba.
