Akalla fursunoni 52 da ke gidajen gyaran hali a Jihar Kano sun fara rubuta jarabawar kammala makarantar sakandare ta shekarar 2026 da Hukumar Shirya Jarabawar Kasa (NECO) da Hukumar Jarabawar Larabci da Addinin Musulunci (NABAIS) ke gudanarwa.
Mai magana da yawun Hukumar Gyaran Hali ta Najeriya reshen Jihar Kano, Musbahu Lawan, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a.
Sanarwar ta ce daga cikin wadanda ke rubuta jarabawar akwai maza 41 da mata 11, wadanda aka zabo daga gidajen gyaran hali daban-daban da ke fadin jihar.
Hukumar ta bayyana cewa shiga jarabawar na daga cikin kokarin da take yi na gyara halayen fursunoni da shirya su domin komawa cikin al’umma ta hanyar ilimi da koyon sana’o’i.
Kwanturola na Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano, Yusuf Lakpene, ya ziyarci cibiyoyin da ake gudanar da jarabawar domin sa ido kan yadda aka fara gudanar da ita.
Yayin da yake jawabi ga fursunonin, Lakpene ya bukace su da su nuna da’a da gaskiya a lokacin rubuta jarabawar, yana mai cewa ilimi na daga cikin hanyoyin da suka fi tasiri wajen sauya rayuwa, rage komawa aikata laifi da kuma shirya mutum ya zama mai amfani ga al’umma bayan kammala zaman gidan gyaran hali.
Ya kuma yabawa gwamnatin Jihar Kano karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa daukar nauyin kudin rajistar jarabawar fursunonin.
A cewarsa, wannan mataki ya nuna kudirin gwamnatin jihar na tabbatar da cewa kowa ya samu damar ilimi, har da mutanen da ke cibiyoyin gyaran hali.
Lakpene ya sake tabbatar da cewa Hukumar Gyaran Hali za ta ci gaba da fadada shirye-shiryen ilimi a gidajen gyaran hali domin inganta ilimi, ci gaban mutum da kuma sauya halayen fursunoni zuwa nagari.
A lokacin ziyarar, Lakpene ya samu rakiyar jami’ai da suka hada da Shugaban Gidan Gyaran Hali na Kurmawa, DCC Ibrahim Rambo; Shugaban Sashen Hukuncin da Ba na Tsare Ba, ACC Musa Muhamma; da kuma Shugaban Makarantar Gidan Gyaran Hali, DSC Ahmad Alkanawi.