Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    KOTU TA SAMU MACE DA LAIFIN YUNKURIN KASHE ƳAR SHEKARA 9 BAYAN TA YAUDARE TA ZUWA DAJI

    June 26, 2026

    KOTU TA KI SAKIN SOWORE, TA DAGE YANKE HUKUNCI ZUWA 30 GA YUNI

    June 24, 2026

    Sarkin Ilorin Ya Taya Musulmi Murnar Sabuwar Shekarar Hijira, Ya Yi Kiran Hadin Kai

    June 16, 2026

    Ranar Dimokuradiyya: SDP Ta Bukaci Shugabanni Su Yi Mulki Da Gaskiya Da Kishin Kasa

    June 12, 2026

    📰 Labarin Yanar Gizo (Hausa Version): Kaduna Pilgrims Board Ya Tabbatar An Yi Hadaya Ga Duk Masu Biyan Kuɗi

    June 9, 2026

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Zafin Rana Mai Tsanani Ya Ɓarke a Turai: Matsalar Heat Dome

    June 30, 2025

    July 3, 2026

    Majalisar Iran Ta Bukaci Jama’a Su Halarci Jana’izar Jagoran Addini Domin Nuna Hadin Kai

    July 2, 2026

    Kalaman Remi Tinubu kan sana’ar ƙosai da gasasshen masara sun jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta

    June 26, 2026

    Gwamnatin Tarayya ta yabawa jakadan Najeriya bayan sakin ‘yan Najeriya da aka tsare a Côte d’Ivoire

    June 26, 2026
  • Asrah 24 TV
  • Education

    NELFUND Na Binciken Makarantu 34 Kan Rashin Mayar Wa Dalibai Kudin Makaranta

    July 6, 2026

    ‘Yar Najeriya Ta Kammala Karatun Likitanci a Rasha da Makin 4.90 CGPA

    July 6, 2026

    Portable Ya Ce Zai Koma Makaranta Domin Kammala Karatunsa

    July 6, 2026

    Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Gudanar da Gwajin Kwarewar Dalibai Duk Bayan Shekaru Uku – Alausa

    July 3, 2026

    Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Sauya Kakin NYSC Da Tufafin Adire

    July 2, 2026
  • Health

    Majalisar Dattawa Ta Gabatar Da Kudirin Kirkirar Tsarin Lafiya Na Zamani Zuwa Karatu Na Biyu

    July 8, 2026

    “Ba Abu Ne Mai Sauƙi Ba” – Wata Uwar da Ta Yi Surrogacy Ta Bayyana Kalubalen da Ta Fuskanta

    July 7, 2026

    Jinyar Mace Ta Karya Al’adar Addinin Buddha Domin Ceto Rayukan Sufaye Bayan Mummunan Hatsari

    July 3, 2026

    Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Karfafa Hadin Gwiwa Da Cibiyoyin Bincike Domin Dakile Barkewar Cututtuka

    July 2, 2026

    TETFund ta ƙalubalanci masana kimiyya su gaggauta samar da rigakafin cutar Lassa Fever na farko a Najeriya

    June 30, 2026
  • Podcast
  • Politics

    Tinubu Ya Aika Sunan Lamido Yuguda Domin Shugabancin AMCON

    July 8, 2026

    Majalisar Dattawa Ta Amince Da Nada Dr. Zainab Marwa A Hukumar NDDC

    July 8, 2026

    Rigima Ta Barke A Majalisar Wakilai Kan Bukatar A Gayyaci Tinubu

    July 8, 2026

    Mai Yiwuwa Ba Zan Kai Ga Tsayawa Takarar 2027 Ba cewar Peter Obi

    July 8, 2026

    An Binciki PFIPC: Adeyemi Ya Sha Alwashin Bai Wa ICPC Hadin Kai

    July 8, 2026
  • Sports

    Messi Ya Kafa Sabon Tarihi A Gasar Kofin Duniya Ta FIFA

    July 8, 2026

    Masar Ta Bukaci FIFA Ta Hukunta Alkalan Wasanta Da Argentina

    July 8, 2026

    Yusuf Alli Ya Bukaci ‘Yan Wasan Najeriya Su Zama Masu Ladabi Gabanin Wasannin Commonwealth 2026

    July 6, 2026

    Kwara United Ta Sanya Ranar Komawa Sansani Gabanin Sabon Kakarar NPFL

    July 2, 2026

    Coco Gauff Ta Bayyana Yadda Gwajin Hana Amfani da Kwayoyin Kara Kuzari Ya Taba Sanya Ta Yin Kuka

    July 2, 2026
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home
News

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaJuly 3, 20262 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp

Akalla fursunoni 52 da ke gidajen gyaran hali a Jihar Kano sun fara rubuta jarabawar kammala makarantar sakandare ta shekarar 2026 da Hukumar Shirya Jarabawar Kasa (NECO) da Hukumar Jarabawar Larabci da Addinin Musulunci (NABAIS) ke gudanarwa.

 

Mai magana da yawun Hukumar Gyaran Hali ta Najeriya reshen Jihar Kano, Musbahu Lawan, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a.

Sanarwar ta ce daga cikin wadanda ke rubuta jarabawar akwai maza 41 da mata 11, wadanda aka zabo daga gidajen gyaran hali daban-daban da ke fadin jihar.

Hukumar ta bayyana cewa shiga jarabawar na daga cikin kokarin da take yi na gyara halayen fursunoni da shirya su domin komawa cikin al’umma ta hanyar ilimi da koyon sana’o’i.
Kwanturola na Hukumar Gyaran Hali ta Jihar Kano, Yusuf Lakpene, ya ziyarci cibiyoyin da ake gudanar da jarabawar domin sa ido kan yadda aka fara gudanar da ita.

Yayin da yake jawabi ga fursunonin, Lakpene ya bukace su da su nuna da’a da gaskiya a lokacin rubuta jarabawar, yana mai cewa ilimi na daga cikin hanyoyin da suka fi tasiri wajen sauya rayuwa, rage komawa aikata laifi da kuma shirya mutum ya zama mai amfani ga al’umma bayan kammala zaman gidan gyaran hali.

Ya kuma yabawa gwamnatin Jihar Kano karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa daukar nauyin kudin rajistar jarabawar fursunonin.

A cewarsa, wannan mataki ya nuna kudirin gwamnatin jihar na tabbatar da cewa kowa ya samu damar ilimi, har da mutanen da ke cibiyoyin gyaran hali.

Lakpene ya sake tabbatar da cewa Hukumar Gyaran Hali za ta ci gaba da fadada shirye-shiryen ilimi a gidajen gyaran hali domin inganta ilimi, ci gaban mutum da kuma sauya halayen fursunoni zuwa nagari.

A lokacin ziyarar, Lakpene ya samu rakiyar jami’ai da suka hada da Shugaban Gidan Gyaran Hali na Kurmawa, DCC Ibrahim Rambo; Shugaban Sashen Hukuncin da Ba na Tsare Ba, ACC Musa Muhamma; da kuma Shugaban Makarantar Gidan Gyaran Hali, DSC Ahmad Alkanawi.

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticleJinyar Mace Ta Karya Al’adar Addinin Buddha Domin Ceto Rayukan Sufaye Bayan Mummunan Hatsari
Next Article An Ji Harbe-harbe Tsakanin Al’ummomin Okrika da Eleme Saboda Rikicin Filaye

Related Posts

Majalisar Iran Ta Bukaci Jama’a Su Halarci Jana’izar Jagoran Addini Domin Nuna Hadin Kai

July 2, 2026

Kalaman Remi Tinubu kan sana’ar ƙosai da gasasshen masara sun jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta

June 26, 2026

Gwamnatin Tarayya ta yabawa jakadan Najeriya bayan sakin ‘yan Najeriya da aka tsare a Côte d’Ivoire

June 26, 2026

KOTU TA SAMU MACE DA LAIFIN YUNKURIN KASHE ƳAR SHEKARA 9 BAYAN TA YAUDARE TA ZUWA DAJI

June 26, 2026
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

Ministan Tsaro Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Harbe ’Yan Ta’adda Ba Tare Da Jira Umarni Ba

July 8, 2026

Tinubu Ya Aika Sunan Lamido Yuguda Domin Shugabancin AMCON

July 8, 2026

Messi Ya Kafa Sabon Tarihi A Gasar Kofin Duniya Ta FIFA

July 8, 2026

Sabon Mamban Kwamitin TETFund Ya Yi Alƙawarin Yin Aiki Cikin Gaskiya

July 8, 2026

Majalisar Dattawa Ta Gabatar Da Kudirin Kirkirar Tsarin Lafiya Na Zamani Zuwa Karatu Na Biyu

July 8, 2026
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.