Babban Sakataren Tertiary Education Trust Fund (TETFund), Sonny Echono, ya ƙalubalanci masana kimiyyar Najeriya da su nemo hanya mafi sauri wajen samar da rigakafin cutar Lassa Fever na farko da za a ƙera a ƙasar, yana mai cewa cutar na ci gaba da zama babbar barazana ga lafiyar al’umma.
Echono ya bayyana hakan ne a Abuja yayin karɓar sakamakon wani babban bincike kan cutar Lassa Fever da Jami’ar Federal University of Health Sciences, Otukpo ta gudanar tare da tallafin TETFund.
Ya ce binciken ya nuna cewa lokaci ya yi da Najeriya za ta wuce matakin tattara bayanan kimiyya zuwa samar da hanyoyin magani da kariya da za su amfani rayuwar jama’a kai tsaye.
Ya buƙaci tawagar masu binciken ta mayar da hankali wajen samar da rigakafin cutar, yana mai jaddada cewa rigakafi ita ce hanya mafi inganci wajen dakile yaduwar cututtuka masu yaɗuwa.
Echono ya ce TETFund za ta haɗa kai da Cibiyar Yaƙi da Cututtuka ta Najeriya (NCDC) da Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya domin tabbatar da cewa sakamakon binciken ya zama tushen manufofin kiwon lafiya na ƙasa.
Ya kuma bayyana cewa idan aka tabbatar da ingancin binciken, hakan zai ƙarfafa ƙoƙarin kafa cibiyar samar da rigakafi a Najeriya.
A nasa jawabin, Mataimakin Shugaban Jami’ar, Farfesa Francis Uba, ya ce TETFund ta nuna hangen nesa shekaru huɗu da suka gabata lokacin da ta bai wa jami’ar tallafin bincike na Naira miliyan 250 domin gudanar da wannan bincike.
Ya ce cutar Lassa Fever na ci gaba da kashe mutane tare da jefa tsarin kiwon lafiya da tattalin arzikin Najeriya da sauran ƙasashen Afirka ta Yamma cikin ƙalubale.
Shugaban binciken, Dr. Joseph Okopi, ya bayyana cewa Najeriya ce ƙasar da ta fi fama da cutar Lassa Fever a duniya, inda tsakanin mutane 5,000 zuwa 10,000 ke rasa rayukansu duk shekara.
Ya ce binciken ya gano cewa Jihar Benue ce ta fi yawan masu ɗauke da ƙwayoyin rigakafin cutar a cikin jihohin da aka gudanar da binciken.
Haka kuma ya bayyana cewa manya masu shekaru tsakanin 20 zuwa 40 sun fi fuskantar haɗarin kamuwa da cutar saboda ayyukan noma da sauran ayyukan waje da ke ƙara haɗuwarsu da berayen da ke ɗauke da ƙwayar cutar.
Binciken ya kuma nuna cewa gidaje marasa inganci, yawaitar beraye, gurɓataccen abinci, rufin gidaje masu zubewa da ƙofofi marasa kyau suna daga cikin manyan abubuwan da ke ƙara haɗarin kamuwa da cutar.
Sai dai masu binciken sun ce akasin ra’ayin da mutane da dama suka ɗauka, cin naman bera ba shi ne babban abin da ke haddasa kamuwa da cutar Lassa Fever ba.
A bangaren binciken marasa lafiya, Dr. Audu Onyemocho ya ce an gudanar da bincike kan mutane 1,266, inda aka tabbatar da mutum 43 sun kamu da cutar ta hanyar gwajin kimiyya.
Ya ce zubar jini, tsufa da kuma kamuwa da farfaɗiya su ne manyan abubuwan da ke ƙara haɗarin mutuwa ga masu fama da cutar.
Masana sun kammala da jaddada cewa samar da ingantaccen rigakafin cutar Lassa Fever ya kamata ya kasance babban buri na Najeriya domin rage mace-mace da kuma ƙarfafa tsarin kiwon lafiyar ƙasa.
