Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    KOTU TA SAMU MACE DA LAIFIN YUNKURIN KASHE ƳAR SHEKARA 9 BAYAN TA YAUDARE TA ZUWA DAJI

    June 26, 2026

    KOTU TA KI SAKIN SOWORE, TA DAGE YANKE HUKUNCI ZUWA 30 GA YUNI

    June 24, 2026

    Sarkin Ilorin Ya Taya Musulmi Murnar Sabuwar Shekarar Hijira, Ya Yi Kiran Hadin Kai

    June 16, 2026

    Ranar Dimokuradiyya: SDP Ta Bukaci Shugabanni Su Yi Mulki Da Gaskiya Da Kishin Kasa

    June 12, 2026

    📰 Labarin Yanar Gizo (Hausa Version): Kaduna Pilgrims Board Ya Tabbatar An Yi Hadaya Ga Duk Masu Biyan Kuɗi

    June 9, 2026

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Zafin Rana Mai Tsanani Ya Ɓarke a Turai: Matsalar Heat Dome

    June 30, 2025

    July 3, 2026

    Majalisar Iran Ta Bukaci Jama’a Su Halarci Jana’izar Jagoran Addini Domin Nuna Hadin Kai

    July 2, 2026

    Kalaman Remi Tinubu kan sana’ar ƙosai da gasasshen masara sun jawo ce-ce-ku-ce a kafafen sada zumunta

    June 26, 2026

    Gwamnatin Tarayya ta yabawa jakadan Najeriya bayan sakin ‘yan Najeriya da aka tsare a Côte d’Ivoire

    June 26, 2026
  • Asrah 24 TV
  • Education

    NELFUND Na Binciken Makarantu 34 Kan Rashin Mayar Wa Dalibai Kudin Makaranta

    July 6, 2026

    ‘Yar Najeriya Ta Kammala Karatun Likitanci a Rasha da Makin 4.90 CGPA

    July 6, 2026

    Portable Ya Ce Zai Koma Makaranta Domin Kammala Karatunsa

    July 6, 2026

    Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Gudanar da Gwajin Kwarewar Dalibai Duk Bayan Shekaru Uku – Alausa

    July 3, 2026

    Gwamnatin Tarayya Ta Shirya Sauya Kakin NYSC Da Tufafin Adire

    July 2, 2026
  • Health

    Majalisar Dattawa Ta Gabatar Da Kudirin Kirkirar Tsarin Lafiya Na Zamani Zuwa Karatu Na Biyu

    July 8, 2026

    “Ba Abu Ne Mai Sauƙi Ba” – Wata Uwar da Ta Yi Surrogacy Ta Bayyana Kalubalen da Ta Fuskanta

    July 7, 2026

    Jinyar Mace Ta Karya Al’adar Addinin Buddha Domin Ceto Rayukan Sufaye Bayan Mummunan Hatsari

    July 3, 2026

    Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alkawarin Karfafa Hadin Gwiwa Da Cibiyoyin Bincike Domin Dakile Barkewar Cututtuka

    July 2, 2026

    TETFund ta ƙalubalanci masana kimiyya su gaggauta samar da rigakafin cutar Lassa Fever na farko a Najeriya

    June 30, 2026
  • Podcast
  • Politics

    Tinubu Ya Aika Sunan Lamido Yuguda Domin Shugabancin AMCON

    July 8, 2026

    Majalisar Dattawa Ta Amince Da Nada Dr. Zainab Marwa A Hukumar NDDC

    July 8, 2026

    Rigima Ta Barke A Majalisar Wakilai Kan Bukatar A Gayyaci Tinubu

    July 8, 2026

    Mai Yiwuwa Ba Zan Kai Ga Tsayawa Takarar 2027 Ba cewar Peter Obi

    July 8, 2026

    An Binciki PFIPC: Adeyemi Ya Sha Alwashin Bai Wa ICPC Hadin Kai

    July 8, 2026
  • Sports

    Messi Ya Kafa Sabon Tarihi A Gasar Kofin Duniya Ta FIFA

    July 8, 2026

    Masar Ta Bukaci FIFA Ta Hukunta Alkalan Wasanta Da Argentina

    July 8, 2026

    Yusuf Alli Ya Bukaci ‘Yan Wasan Najeriya Su Zama Masu Ladabi Gabanin Wasannin Commonwealth 2026

    July 6, 2026

    Kwara United Ta Sanya Ranar Komawa Sansani Gabanin Sabon Kakarar NPFL

    July 2, 2026

    Coco Gauff Ta Bayyana Yadda Gwajin Hana Amfani da Kwayoyin Kara Kuzari Ya Taba Sanya Ta Yin Kuka

    July 2, 2026
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home » Bincike Ya Nuna Ta’addanci Da Rikicin Manoma Da Makiyaya Na Kara Talauta Al’ummar Arewacin Najeriya
Security

Bincike Ya Nuna Ta’addanci Da Rikicin Manoma Da Makiyaya Na Kara Talauta Al’ummar Arewacin Najeriya

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaJune 18, 20263 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp
135e9980 b8ba 11f0 aa13 0b0479f6f42a.png

Wani sabon bincike ya bayyana cewa matsalolin tsaro da suka hada da ta’addanci, rikicin manoma da makiyaya da kuma sace-sacen mutane na kara jefa al’ummar Arewacin Najeriya cikin talauci tare da rage karfin iyalai na farfadowa daga matsin tattalin arziki.

Rahoton mai taken “Insecurity, Livelihoods and Welfare in Northern Nigeria” ya gano manyan matsalolin tsaro guda uku da suka fi addabar yankin Arewa. Wadannan sun hada da hare-haren Boko Haram da ISWAP a Arewa maso Gabas, rikicin manoma da makiyaya a Arewa ta Tsakiya da kuma ayyukan ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane a Arewa maso Yamma.

An bayyana sakamakon binciken ne a wani taron yanar gizo da aka gudanar a Abuja, wanda cibiyar Chronic Poverty Advisory Network (CPAN) ta kasar Birtaniya, Development Research and Projects Centre (dRPC) da kuma shirin Strengthening Peace and Resilience in Nigeria (SPRiNG) suka shirya.

Ministan Harkokin Jin Kai da Rage Talauci, Dakta Bernard Doro, ya halarci taron inda ya yi tsokaci kan muhimmancin sakamakon binciken ga manufofin gwamnati na yaki da talauci.

Yayin gabatar da rahoton, Mataimakiyar Daraktan CPAN, Dakta Vidya Diwakar, ta bayyana cewa binciken ya yi amfani da bayanai daga binciken rayuwar al’umma na Najeriya na shekarar 2022/2023, binciken lafiya da al’umma na 2024 da kuma bayanan rikice-rikice daga shekarar 2010 zuwa 2025.

Rahoton ya nuna cewa iyalan da hare-haren Boko Haram da ISWAP suka shafa a Arewa maso Gabas sun samu raguwar kashe-kashen rayuwa da kashi tsakanin takwas zuwa 14 cikin dari idan aka kwatanta da sauran gidaje.

Haka kuma, bashin da ya samo asali daga rikice-rikice tun daga shekarar 2009 ya kara janyo asarar kudaden rayuwa da kashi tsakanin takwas zuwa 13 cikin dari.

Binciken ya kuma gano cewa rikicin manoma da makiyaya a Arewa ta Tsakiya shi ne ya fi haddasa mummunan tasiri ga iyalan da ke kusa da layin talauci, inda aka samu raguwar kudaden rayuwa da kashi 14 cikin dari.

A Arewa maso Yamma kuwa, ayyukan ‘yan bindiga da garkuwa da mutane sun haddasa asarar kudaden rayuwa da ke tsakanin kashi hudu zuwa 11 cikin dari, musamman ga gidajen da ke fama da matsakaicin talauci.

Sai dai rahoton ya bayyana cewa hada hanyoyin samun kudin shiga daban-daban ita ce hanya mafi tasiri wajen taimakawa iyalai su jure kalubalen talauci da rikice-rikice.

Binciken ya nuna cewa hada noma, sana’o’in hannu da sauran harkokin kasuwanci na taimakawa wajen kare iyalai daga fadawa cikin matsanancin talauci.

Duk da haka, rahoton ya nuna cewa kashi 13 cikin dari kacal na shugabannin gidaje a Arewacin Najeriya ne ke da hanyoyin samun kudin shiga fiye da daya.

Masana da suka yi sharhi kan binciken sun jaddada muhimmancin hada kokarin samar da zaman lafiya da shirye-shiryen farfado da hanyoyin samun abin rayuwa domin rage talauci da karfafa zaman lafiya mai dorewa.

Sun kuma bukaci a kara horas da sarakunan gargajiya da shugabannin al’umma domin su taka muhimmiyar rawa wajen sasanta rikice-rikice da inganta zaman lafiya a yankunansu.

A karshen taron, gwamnatin tarayya ta yi alkawarin ci gaba da hada kai da masu ruwa da tsaki wajen aiwatar da manufofin rage talauci tare da amfani da bincike da hujjoji wajen tsara shirye-shiryen da za su amfani mata da matasa, wadanda galibi ke fuskantar kalubalen samun tallafi.

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticleNajeriya Na Iya Daukar Mataki Kan Kamfanonin Afirka Ta Kudu – Bianca Ojukwu
Next Article Bankin Zuba Jari Na Turai Da DBN Sun Kulla Yarjejeniyar Tallafin Yuro Miliyan 200 Ga Kananan Kasuwanci A Najeriya

Related Posts

Ministan Tsaro Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Harbe ’Yan Ta’adda Ba Tare Da Jira Umarni Ba

July 8, 2026

‘Yan Sanda Sun Kwace Motoci 195 Kan Laifin Lambobin Rajista a Enugu

July 8, 2026

‘Yan Bindiga Sun Sace Daliban Jami’ar Lafia Uku, ‘Yan Sanda Sun Ceto Daya

July 8, 2026

Rundunar ‘Yan Sandan Ebonyi Ta Tsare Jami’ai Kan Zargin Dukan Wani Farar Hula

July 7, 2026
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

Ministan Tsaro Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Harbe ’Yan Ta’adda Ba Tare Da Jira Umarni Ba

July 8, 2026

Tinubu Ya Aika Sunan Lamido Yuguda Domin Shugabancin AMCON

July 8, 2026

Messi Ya Kafa Sabon Tarihi A Gasar Kofin Duniya Ta FIFA

July 8, 2026

Sabon Mamban Kwamitin TETFund Ya Yi Alƙawarin Yin Aiki Cikin Gaskiya

July 8, 2026

Majalisar Dattawa Ta Gabatar Da Kudirin Kirkirar Tsarin Lafiya Na Zamani Zuwa Karatu Na Biyu

July 8, 2026
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.