Gwamnatin Jihar Neja ta bukaci mazauna jihar da su ci gaba da harkokinsu na yau da kullum tare da yin watsi da rahotannin da ke yawo kan cewa ’yan bindiga sun kai hare-hare a Minna da wasu yankuna na jihar.
Kwamishinan Yada Labarai da Wayar da Kai na jihar, Obed Nana, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya tabbatar wa iyaye, malamai da dalibai cewa jihar Neja na cikin zaman lafiya kuma makarantu na ci gaba da gudanar da ayyukansu cikin tsaro.
Sanarwar ta zo ne bayan wasu rahotanni da suka bazu a kafafen sada zumunta suna ikirarin cewa an kai hare-hare a wasu makarantu da ke Bosso, Kpakungu, Sabon-Wuse, Lambata da sauran yankuna, tare da sace dalibai da malamai.
Rahotannin sun haddasa fargaba a wasu makarantu, lamarin da ya sa aka rufe wasu daga cikinsu cikin gaggawa tare da sallamar dalibai da malamai zuwa gidajensu.
Sai dai Kwamishinan ya ce bayan tuntubar Ma’aikatar Ilimin Firamare da Sakandare, Rundunar ’Yan Sanda da sauran hukumomin tsaro, an tabbatar da cewa babu wani irin hari da ya faru a wuraren da aka ambata.
Ya bayyana cewa rahotannin karya ne da aka kirkira domin haddasa tsoro da rudani a tsakanin al’umma.
Nana ya kara da cewa gwamnatin jihar na ci gaba da aiki kafada da kafada da jami’an tsaro, shugabannin makarantu da sauran masu ruwa da tsaki domin karfafa tsaro a makarantu da kewaye da su.
Haka kuma ya bukaci iyaye da masu kula da yara da su kwantar da hankalinsu tare da ci gaba da tura ’ya’yansu makaranta, yana mai tabbatar da cewa an dauki matakan kare rayuka da dukiyoyi.
A nasa bangaren, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Neja, Adamu Elleman, ya umurci jami’an ’yan sanda na yankuna daban-daban da su kara hada kai da shugabannin makarantu domin tabbatar da tsaro.
Rundunar ta kuma bukaci jama’a da su rika kai rahoton duk wani abu da suka gani mai kama da barazana ga tsaro domin daukar matakin gaggawa. O
