Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    Najeriya Ta Kai Dala $18.4 Biliyan a Cinikayyar Cikin Afirka a 2024

    June 28, 2025

    Afreximbank Ta Ba Najeriya Tallafin $50 Biliyan Don Manyan Ayyuka

    June 28, 2025

    Mutane 28 sun mutu sakamakon gudun wuce sa’a a jihar Ondo- FRSC

    February 2, 2025

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Zafin Rana Mai Tsanani Ya Ɓarke a Turai: Matsalar Heat Dome

    June 30, 2025

    Najeriya Ta Samu Jarin Waje Har Dala Biliyan 2.5 Daga Masarautar Saudiyya

    June 29, 2025

    Tiwa Savage Ta Bayyana Yadda Take Rashin Kulawar Don Jazzy Da Mavin

    May 20, 2026

    NERC Da ONSA Sun Hada Kai Don Dakile Lalata Kayan Wutar Lantarki

    May 20, 2026

    Iran Ta Shirya Auren Jama’a Ga Masu Shirin Sadaukar Da Rayukansu A Yaki

    May 19, 2026

    NUJ-FCT Ta Gargadi ‘Yan Jarida Kan Yada Labaran Karya Gabanin Zabuka

    May 19, 2026
  • Asrah 24 TV
  • Education

    Sojojin Najeriya Sun Yaye Sabbin Paratroopers Bayan Kammala Horon Tsalle Daga Jirgin Sama

    June 5, 2026

    Achievers University Ta Bankado Zargin Damfarar Kudin Makaranta Ta N457.5m

    May 25, 2026

    NYSC ta shawarci iyaye su taimaka wa ‘ya’yansu da karin kudin tafiya

    May 21, 2026

    NYSC ta tsawaita wa wasu masu bautar kasa hidima a Gombe

    May 21, 2026

    Najeriya da Italiya sun hada kai domin tara dala biliyan 5 don tallafa wa ilimi

    May 21, 2026
  • Health

    OYO TA KWANTAR WA MAZAUNA HANKALI KAN CUTAR EBOLA, TA SA MA’AIKATAN LAFIYA CIKIN SHIRI

    June 4, 2026

    Likitan Ondo Sun Ƙara Matsin Lamba Kan Gwamnati, Sun Yi Barazanar Tsunduma Yajin Aiki

    May 19, 2026

    Coroner’s Court ta dakatar da shari’ar mutuwar ɗan Chimamanda Adichie har sai umarnin Attorney-General

    May 5, 2026

    Sarki Charles III Ya Yarda Cewa Ciwon Kansar Da Ke Damunsa Na Iya Hana Shi Ganin Dogon Aikin Da Ya Kafa

    April 30, 2026

    Masana lafiya sun bukaci daukar matakin gaggawa kan cutar sickle cell a Najeriya da Afirka

    April 29, 2026
  • Podcast
  • Politics

    Tinubu Torchbearers Zai Taimaka Wajen Wayar Da Kai Da Tallafawa Gwamnati — APC Women Leader

    June 4, 2026

    INEC Ta Shirya Tsaf Domin Zaben Sanatan Ondo Kudu Ranar 20 ga Yuni

    June 4, 2026

    LP Ta Kammala Zaben Fidda Gwani, Ta Tsayar da ‘Yan Takara na Majalisa a Anambra

    June 4, 2026

    Peter Obi Ya Kare Adeboye, Ya Gargadi Matasa Kan Rarrabuwar Kabilanci Da Addini

    June 4, 2026

    Tsohon Firaministan Senegal Ousmane Sonko Ya Zama Kakakin Majalisa

    May 26, 2026
  • Sports

    Shaibu Ya Yabawa Super Eagles Da Adeboye Kan Nasarorin Unity Cup Da Wasan Poland

    June 4, 2026

    Super Eagles Na Da Ƙarfin Doke Kowace Ƙasa Duk Da Rashin Tikitin Gasar Kofin Duniya

    June 4, 2026

    Kai Havertz Ya Yabawa Jamus Karfin ‘Yan Hari Gaban Gasar Kofin Duniya Ta 2026

    June 4, 2026

    Marinakis Ya Yi Rikici A Athens Yayin Gasar EuroLeague

    May 25, 2026

    Spurs Sun Farfado Thunder, Wembanyama Ya Jagoranci Nasara A Wasan NBA

    May 25, 2026
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home » Najeriya da Italiya sun hada kai domin tara dala biliyan 5 don tallafa wa ilimi
Education

Najeriya da Italiya sun hada kai domin tara dala biliyan 5 don tallafa wa ilimi

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaMay 21, 20262 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp
Nigeria Italy 750x536

Kasashen Najeriya da Italiya sun amince da kafa kwamitin hadin gwiwa domin gudanar da wani sabon gangamin samar da kudade na ilimi karkashin shirin Global Partnership for Education (GPE), da nufin tara dala biliyan 5 kafin taron ilimi na duniya da za a gudanar a birnin Rome na kasar Italiya a watan Satumban 2026.

Shirin mai suna “Multiply Possibility Campaign” na da burin inganta damar ilimi ga kimanin yara miliyan 750 a duniya tare da samar da karin dala biliyan 10 na tallafin cikin gida ga bangaren ilimi nan da shekarar 2030.

Ministar harkokin wajen Najeriya, Ambasada Bianca Odumegwu-Ojukwu, ce ta bayyana hakan yayin wata ganawa da jakadan Italiya a Najeriya, Roberto Mengoni, a Abuja ranar Laraba.

A cewarta, hadin gwiwar ya dace da manufofin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na “Renewed Hope Agenda,” musamman ganin yawan matasan Najeriya da bukatar saka hannun jari a bangaren ilimi.

Ta bayyana cewa taron da gangamin tara kudaden za su taimaka wajen bai wa matasa kwarewa, samar musu da ayyukan yi da kuma rage matsalar hijira zuwa kasashen waje.

“Wannan hadin gwiwa zai taimaka wajen bai wa matasa ilimi da kwarewa tare da samar da ayyukan yi da kuma rage hijira,” in ji Odumegwu-Ojukwu.

Ministar ta kuma bukaci kasashen biyu su kara hada kai wajen magance matsalolin hijira cikin fahimta da hadin kai, tana mai jaddada kudirin Najeriya na karfafa dangantaka da Italiya.

Ta kara da cewa gwamnatin tarayya na duba hanyoyin zuba jari a bangaren kare muhalli musamman a yankunan da ke fuskantar matsaloli.

Tun da farko, Jakadan Italiya Roberto Mengoni ya ce ganawar tana da muhimmanci domin kasashen biyu su cimma matsaya kan shirye-shiryen taron ilimi na duniya da za a gudanar a Rome a watan Satumban 2026.

Ya ce baya ga ilimi, kasashen biyu sun tattauna kan harkokin yawon bude ido, tattalin arziki da kuma hadin gwiwar tsaro tsakanin Najeriya da Italiya.

Ana sa ran taron ilimi na duniya zai hada gwamnatoci da kungiyoyin ci gaba da sauran masu ruwa da tsaki domin samar da tallafi da kudade wajen bunkasa ingantaccen ilimi a duniya.

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticleMagoya bayan APC a Bauchi sun yi watsi da yunkurin kakaba dan takarar gwamna
Next Article Oyo Ta Musanta Rahotannin Sakin Dalibai Da Malaman Da Aka Sace A Ogbomoso

Related Posts

Sojojin Najeriya Sun Yaye Sabbin Paratroopers Bayan Kammala Horon Tsalle Daga Jirgin Sama

June 5, 2026

Achievers University Ta Bankado Zargin Damfarar Kudin Makaranta Ta N457.5m

May 25, 2026

NYSC ta shawarci iyaye su taimaka wa ‘ya’yansu da karin kudin tafiya

May 21, 2026

NYSC ta tsawaita wa wasu masu bautar kasa hidima a Gombe

May 21, 2026
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

Mummunar Hanyar Kauye Na Hana Yara Zuwa Makaranta A Akwa Ibom — Mazauna Yanki

June 5, 2026

Sojojin Najeriya Sun Yaye Sabbin Paratroopers Bayan Kammala Horon Tsalle Daga Jirgin Sama

June 5, 2026

Dayo Amusa Ta Soki Matsin Lambar Da Ake Yi Wa Fitattun Jarumai Kan Matsalolin Kasa

June 5, 2026

Kungiya Ta Bukaci Hadin Kan ‘Yan Najeriya Wajen Yaki Da Matsalar Tsaro

June 5, 2026

TCN Ta Sanar da Katse Wutar Lantarki a Sassan Delta Saboda Ayyukan Gyaran Tashar Wuta

June 5, 2026
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.