Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    CBN Ta Ce Sauye-Sauyen Tattalin Arziki Sun Kafa Tubalin Ci Gaba Da Daidaiton Arzikin Najeriya

    August 6, 2026

    KOTU TA SAMU MACE DA LAIFIN YUNKURIN KASHE ƳAR SHEKARA 9 BAYAN TA YAUDARE TA ZUWA DAJI

    June 26, 2026

    KOTU TA KI SAKIN SOWORE, TA DAGE YANKE HUKUNCI ZUWA 30 GA YUNI

    June 24, 2026

    Sarkin Ilorin Ya Taya Musulmi Murnar Sabuwar Shekarar Hijira, Ya Yi Kiran Hadin Kai

    June 16, 2026

    Hukumar Kula da Mahajjatan Kano Ta Kayyade 25 ga Agusta a Matsayin Ranar Ƙarshe ta Miƙa Fasfo

    August 8, 2026

    📰 Labarin Yanar Gizo (Hausa Version): Kaduna Pilgrims Board Ya Tabbatar An Yi Hadaya Ga Duk Masu Biyan Kuɗi

    June 9, 2026

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Hukumar Kula da Mahajjatan Kano Ta Kayyade 25 ga Agusta a Matsayin Ranar Ƙarshe ta Miƙa Fasfo

    August 8, 2026

    Baturen Spain Ya Zo Legas Neman Masu Damfarar Mahaifiyarsa Ta Soyayya

    August 8, 2026

    CBN Ta Ce Sauye-Sauyen Tattalin Arziki Sun Kafa Tubalin Ci Gaba Da Daidaiton Arzikin Najeriya

    August 6, 2026

    Trump Ya Bukaci Kamfanonin Mai Su Rage Farashin Mai Bayan Zargin Samun Ribar Da Ta Yi Yawa

    August 5, 2026
  • Asrah 24 TV
  • Education

    Farfesa Oloyede Ya Ajiye Muƙaminsa a JAMB Bayan Shekaru 10, Ya Koma Koyarwa

    July 31, 2026

    Ɗalibin UNILAG Ya Lashe Gasar Huawei ta ICT ta Duniya a China

    July 31, 2026

    Yajin Aikin ASUU Ya Jefa Daliban Jami’ar AAUA Cikin Rashin Tabbas

    July 27, 2026

    Save the Children Ta Mara Wa Kaduna Baya Don Mayar Da Yara 100,000 Makaranta

    July 24, 2026

    ‘Yar Ministan Abuja Nyesom Wike Ta Samu Digirin Lauya A Birtaniya

    July 22, 2026
  • Health

    ICPC Ta Gurfanar da Likitan El-Rufai Kan Zargin Ƙirƙirar Rahoton Lafiya na Karya Domin Neman Beli

    July 20, 2026

    Masana Sun Yi Gargadin Cewa Gano Cutar Sarcoma Da Wuri Na Iya Taimakawa Wajen Ceto Rayuka

    July 16, 2026

    Kusan Kashi 45% Na Cutar Dementia Ana Iya Hana Ta Ta Hanyar Canza Salon Rayuwa

    July 15, 2026

    Yobe, Qatar Charity Sun Kaddamar da Shirin Kyauta na Duba Ido da Aikin Cataract

    July 15, 2026

    Shahararren Mai Binciken Abinci, Opeyemi Famakin, Ya Ba Da Labarin Yadda Aikin 9-zuwa-5 Ya Gina Rayuwarsa

    July 13, 2026
  • Podcast
  • Politics

    APC Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Ya Nemi Kudancin Kaduna Su Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu Da Uba Sani

    August 8, 2026

    APGA Candidate Ya Janye Waɗa, Ya Goyi Bayan Oyebamiji Na APC

    August 8, 2026

    Uzodimma Ya Mayar Wa Davido Martani Kan Zaɓen Gwamnan Osun

    August 6, 2026

    Zaɓen 15 Ga Agusta Zai Isar Da Saƙo Ga APC – Gwamna Adeleke

    August 6, 2026

    Gwamnatin Tarayya Za Ta Gina Hasumiyoyin Sadarwa 3,700 Domin Haɗa Fiye Da Mutane Miliyan 20 Da Intanet

    August 5, 2026
  • Sports

    Kungiyoyin Premier League Na Gaggawar Kammala Sayayya Kafin Rufe Kasuwar ’Yan Wasa

    August 8, 2026

    Chelsea Ta Lallasa AC Milan 3-0, Ta Lashe Kofin Indonesia Super Cup

    August 8, 2026

    Kasashe 13 Sun Janye Goyon Bayan Infantino Gabanin Zaben Shugabancin FIFA na 2027

    August 8, 2026

    NANS Ta Bukaci ‘Yan Arewa Su Guji Siyasantar Da Gyaran Tsarin Fitar Da Fasfo

    August 6, 2026

    Usyk Ya Bayyana Dangantakarsa Da Anthony Joshua, Ya Goyi Bayan Nasararsa Kan Tyson Fury

    August 2, 2026
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home » Magoya bayan APC a Bauchi sun yi watsi da yunkurin kakaba dan takarar gwamna
Politics

Magoya bayan APC a Bauchi sun yi watsi da yunkurin kakaba dan takarar gwamna

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaMay 21, 20263 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp
APC 712x536

Wasu magoya bayan jam’iyyar APC a jihar Bauchi sun yi watsi da zargin yunkurin kakaba dan takarar gwamna kafin gudanar da zaben fidda gwani na jam’iyyar, inda suka bukaci a gudanar da sahihin zabe cikin gaskiya da adalci.

Masu ruwa da tsakin jam’iyyar sun bayyana matsayinsu ne a ranar Alhamis yayin wata ziyara da suka kai otal din da aka sauke kwamitin zaben APC domin neman karin bayani kan jinkirta zaben fidda gwani na gwamna.

Wani jigo a APC, Musa Buba Mohammed wanda aka fi sani da “Civilian General,” ya ce mambobin jam’iyyar ba za su amince da kokarin wasu tsirarun mutane na kakaba musu dan takara ba.

Ya ce dimokuradiyya dole ta kasance bisa ra’ayin mambobin jam’iyya ba wai anfani na wasu kalilan ba.

“Mun zo ne domin bayyana korafinmu saboda dimokuradiyya gwamnati ce ta jama’a, daga jama’a kuma domin jama’a, ba gwamnati ta wasu tsiraru ba,” in ji shi.

Mohammed ya ce magoya bayan APC a Bauchi suna bukatar zabe mai gaskiya da adalci wanda zai samar da dan takarar da mambobin jam’iyya da al’umma za su amince da shi.

Ya kara da cewa duk da an dage zaben daga ranar Alhamis zuwa Juma’a, har yanzu suna da fatan za a gudanar da zaben cikin gaskiya.

A cewarsa, magoya bayan jam’iyyar na da yakinin cewa dan takara Nura Manu Soro zai samu nasara idan aka samar da yanayi mai adalci ga kowa.

Ya kuma yi kira ga shugabannin APC da Shugaba Bola Ahmed Tinubu da su tabbatar da gaskiya da adalci a tsarin zaben.

Mohammed ya ce dage zabukan fidda gwani a Bauchi da Kwara ya jefa shakku a zukatan mambobin jam’iyyar, inda mutane da dama ke zargin akwai yunkurin magudi.

“Me yasa aka dage zaben? Dole akwai wani dalili a bayan hakan. Sauran jihohi sun gudanar da zabensu amma Bauchi da Kwara aka dage. Wannan ne ya sa mutane ke fara zargin akwai wata manufa,” ya bayyana.

Ya kara da cewa mambobin jam’iyyar sun samu bayanin dage zaben amma sun dage cewa sai an gudanar da sahihin zabe ne kawai za a ci gaba da samun amincewa da jam’iyyar.

Mohammed ya kuma bayyana cewa APC dole ta kare tsarin dimokuradiyya a cikinta, yana mai cewa Shugaba Tinubu ma ta hanyar zabe ya samu tikiti ba ta hanyar maslaha ba.

“Shugaban kasa ta hanyar kuri’a ya samu nasara, ba ta hanyar yarjejeniya ba. Wannan irin tsarin dimokuradiyya muke bukata a Bauchi,” in ji shi.

Shi ma wani mamba a jam’iyyar, Kwamared Abdul’Aziz Nasrullah, ya bukaci a gudanar da sahihin tsari, yana mai cewa Bauchi na bukatar nagartattun ‘yan takara masu wakiltar muradun jama’a.

Ya yi gargadin cewa kakaba dan takara na iya haddasa rabuwar kai a cikin jam’iyyar.

Dukkan bangarorin biyu sun jaddada biyayyarsu ga APC amma suka ce dole ne a tabbatar da gaskiya, adalci da rikon amana a zaben fidda gwani na gwamna a jihar Bauchi.

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticlePDP ta tsayar da Richard Akinaka takarar Sanatan Bayelsa ta Tsakiya
Next Article Najeriya da Italiya sun hada kai domin tara dala biliyan 5 don tallafa wa ilimi

Related Posts

APC Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Ya Nemi Kudancin Kaduna Su Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu Da Uba Sani

August 8, 2026

APGA Candidate Ya Janye Waɗa, Ya Goyi Bayan Oyebamiji Na APC

August 8, 2026

Uzodimma Ya Mayar Wa Davido Martani Kan Zaɓen Gwamnan Osun

August 6, 2026

Zaɓen 15 Ga Agusta Zai Isar Da Saƙo Ga APC – Gwamna Adeleke

August 6, 2026
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

APC Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Ya Nemi Kudancin Kaduna Su Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu Da Uba Sani

August 8, 2026

APGA Candidate Ya Janye Waɗa, Ya Goyi Bayan Oyebamiji Na APC

August 8, 2026

Kada Ku Hana Amarenku Abinci” – Gwamnan Kano Ya Buƙaci Mazajen Da Suka Amfana Da Auren Gata

August 8, 2026

Hukumar Kula da Mahajjatan Kano Ta Kayyade 25 ga Agusta a Matsayin Ranar Ƙarshe ta Miƙa Fasfo

August 8, 2026

Kungiyoyin Premier League Na Gaggawar Kammala Sayayya Kafin Rufe Kasuwar ’Yan Wasa

August 8, 2026
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.