Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    Najeriya Ta Kai Dala $18.4 Biliyan a Cinikayyar Cikin Afirka a 2024

    June 28, 2025

    Afreximbank Ta Ba Najeriya Tallafin $50 Biliyan Don Manyan Ayyuka

    June 28, 2025

    Mutane 28 sun mutu sakamakon gudun wuce sa’a a jihar Ondo- FRSC

    February 2, 2025

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Zafin Rana Mai Tsanani Ya Ɓarke a Turai: Matsalar Heat Dome

    June 30, 2025

    Najeriya Ta Samu Jarin Waje Har Dala Biliyan 2.5 Daga Masarautar Saudiyya

    June 29, 2025

    Tiwa Savage Ta Bayyana Yadda Take Rashin Kulawar Don Jazzy Da Mavin

    May 20, 2026

    NERC Da ONSA Sun Hada Kai Don Dakile Lalata Kayan Wutar Lantarki

    May 20, 2026

    Iran Ta Shirya Auren Jama’a Ga Masu Shirin Sadaukar Da Rayukansu A Yaki

    May 19, 2026

    NUJ-FCT Ta Gargadi ‘Yan Jarida Kan Yada Labaran Karya Gabanin Zabuka

    May 19, 2026
  • Asrah 24 TV
  • Education

    Sojojin Najeriya Sun Yaye Sabbin Paratroopers Bayan Kammala Horon Tsalle Daga Jirgin Sama

    June 5, 2026

    Achievers University Ta Bankado Zargin Damfarar Kudin Makaranta Ta N457.5m

    May 25, 2026

    NYSC ta shawarci iyaye su taimaka wa ‘ya’yansu da karin kudin tafiya

    May 21, 2026

    NYSC ta tsawaita wa wasu masu bautar kasa hidima a Gombe

    May 21, 2026

    Najeriya da Italiya sun hada kai domin tara dala biliyan 5 don tallafa wa ilimi

    May 21, 2026
  • Health

    OYO TA KWANTAR WA MAZAUNA HANKALI KAN CUTAR EBOLA, TA SA MA’AIKATAN LAFIYA CIKIN SHIRI

    June 4, 2026

    Likitan Ondo Sun Ƙara Matsin Lamba Kan Gwamnati, Sun Yi Barazanar Tsunduma Yajin Aiki

    May 19, 2026

    Coroner’s Court ta dakatar da shari’ar mutuwar ɗan Chimamanda Adichie har sai umarnin Attorney-General

    May 5, 2026

    Sarki Charles III Ya Yarda Cewa Ciwon Kansar Da Ke Damunsa Na Iya Hana Shi Ganin Dogon Aikin Da Ya Kafa

    April 30, 2026

    Masana lafiya sun bukaci daukar matakin gaggawa kan cutar sickle cell a Najeriya da Afirka

    April 29, 2026
  • Podcast
  • Politics

    Tinubu Torchbearers Zai Taimaka Wajen Wayar Da Kai Da Tallafawa Gwamnati — APC Women Leader

    June 4, 2026

    INEC Ta Shirya Tsaf Domin Zaben Sanatan Ondo Kudu Ranar 20 ga Yuni

    June 4, 2026

    LP Ta Kammala Zaben Fidda Gwani, Ta Tsayar da ‘Yan Takara na Majalisa a Anambra

    June 4, 2026

    Peter Obi Ya Kare Adeboye, Ya Gargadi Matasa Kan Rarrabuwar Kabilanci Da Addini

    June 4, 2026

    Tsohon Firaministan Senegal Ousmane Sonko Ya Zama Kakakin Majalisa

    May 26, 2026
  • Sports

    Shaibu Ya Yabawa Super Eagles Da Adeboye Kan Nasarorin Unity Cup Da Wasan Poland

    June 4, 2026

    Super Eagles Na Da Ƙarfin Doke Kowace Ƙasa Duk Da Rashin Tikitin Gasar Kofin Duniya

    June 4, 2026

    Kai Havertz Ya Yabawa Jamus Karfin ‘Yan Hari Gaban Gasar Kofin Duniya Ta 2026

    June 4, 2026

    Marinakis Ya Yi Rikici A Athens Yayin Gasar EuroLeague

    May 25, 2026

    Spurs Sun Farfado Thunder, Wembanyama Ya Jagoranci Nasara A Wasan NBA

    May 25, 2026
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home » Magoya bayan APC a Bauchi sun yi watsi da yunkurin kakaba dan takarar gwamna
Politics

Magoya bayan APC a Bauchi sun yi watsi da yunkurin kakaba dan takarar gwamna

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaMay 21, 20263 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp
APC 712x536

Wasu magoya bayan jam’iyyar APC a jihar Bauchi sun yi watsi da zargin yunkurin kakaba dan takarar gwamna kafin gudanar da zaben fidda gwani na jam’iyyar, inda suka bukaci a gudanar da sahihin zabe cikin gaskiya da adalci.

Masu ruwa da tsakin jam’iyyar sun bayyana matsayinsu ne a ranar Alhamis yayin wata ziyara da suka kai otal din da aka sauke kwamitin zaben APC domin neman karin bayani kan jinkirta zaben fidda gwani na gwamna.

Wani jigo a APC, Musa Buba Mohammed wanda aka fi sani da “Civilian General,” ya ce mambobin jam’iyyar ba za su amince da kokarin wasu tsirarun mutane na kakaba musu dan takara ba.

Ya ce dimokuradiyya dole ta kasance bisa ra’ayin mambobin jam’iyya ba wai anfani na wasu kalilan ba.

“Mun zo ne domin bayyana korafinmu saboda dimokuradiyya gwamnati ce ta jama’a, daga jama’a kuma domin jama’a, ba gwamnati ta wasu tsiraru ba,” in ji shi.

Mohammed ya ce magoya bayan APC a Bauchi suna bukatar zabe mai gaskiya da adalci wanda zai samar da dan takarar da mambobin jam’iyya da al’umma za su amince da shi.

Ya kara da cewa duk da an dage zaben daga ranar Alhamis zuwa Juma’a, har yanzu suna da fatan za a gudanar da zaben cikin gaskiya.

A cewarsa, magoya bayan jam’iyyar na da yakinin cewa dan takara Nura Manu Soro zai samu nasara idan aka samar da yanayi mai adalci ga kowa.

Ya kuma yi kira ga shugabannin APC da Shugaba Bola Ahmed Tinubu da su tabbatar da gaskiya da adalci a tsarin zaben.

Mohammed ya ce dage zabukan fidda gwani a Bauchi da Kwara ya jefa shakku a zukatan mambobin jam’iyyar, inda mutane da dama ke zargin akwai yunkurin magudi.

“Me yasa aka dage zaben? Dole akwai wani dalili a bayan hakan. Sauran jihohi sun gudanar da zabensu amma Bauchi da Kwara aka dage. Wannan ne ya sa mutane ke fara zargin akwai wata manufa,” ya bayyana.

Ya kara da cewa mambobin jam’iyyar sun samu bayanin dage zaben amma sun dage cewa sai an gudanar da sahihin zabe ne kawai za a ci gaba da samun amincewa da jam’iyyar.

Mohammed ya kuma bayyana cewa APC dole ta kare tsarin dimokuradiyya a cikinta, yana mai cewa Shugaba Tinubu ma ta hanyar zabe ya samu tikiti ba ta hanyar maslaha ba.

“Shugaban kasa ta hanyar kuri’a ya samu nasara, ba ta hanyar yarjejeniya ba. Wannan irin tsarin dimokuradiyya muke bukata a Bauchi,” in ji shi.

Shi ma wani mamba a jam’iyyar, Kwamared Abdul’Aziz Nasrullah, ya bukaci a gudanar da sahihin tsari, yana mai cewa Bauchi na bukatar nagartattun ‘yan takara masu wakiltar muradun jama’a.

Ya yi gargadin cewa kakaba dan takara na iya haddasa rabuwar kai a cikin jam’iyyar.

Dukkan bangarorin biyu sun jaddada biyayyarsu ga APC amma suka ce dole ne a tabbatar da gaskiya, adalci da rikon amana a zaben fidda gwani na gwamna a jihar Bauchi.

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticlePDP ta tsayar da Richard Akinaka takarar Sanatan Bayelsa ta Tsakiya
Next Article Najeriya da Italiya sun hada kai domin tara dala biliyan 5 don tallafa wa ilimi

Related Posts

Tinubu Torchbearers Zai Taimaka Wajen Wayar Da Kai Da Tallafawa Gwamnati — APC Women Leader

June 4, 2026

INEC Ta Shirya Tsaf Domin Zaben Sanatan Ondo Kudu Ranar 20 ga Yuni

June 4, 2026

LP Ta Kammala Zaben Fidda Gwani, Ta Tsayar da ‘Yan Takara na Majalisa a Anambra

June 4, 2026

Peter Obi Ya Kare Adeboye, Ya Gargadi Matasa Kan Rarrabuwar Kabilanci Da Addini

June 4, 2026
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

Mummunar Hanyar Kauye Na Hana Yara Zuwa Makaranta A Akwa Ibom — Mazauna Yanki

June 5, 2026

Sojojin Najeriya Sun Yaye Sabbin Paratroopers Bayan Kammala Horon Tsalle Daga Jirgin Sama

June 5, 2026

Dayo Amusa Ta Soki Matsin Lambar Da Ake Yi Wa Fitattun Jarumai Kan Matsalolin Kasa

June 5, 2026

Kungiya Ta Bukaci Hadin Kan ‘Yan Najeriya Wajen Yaki Da Matsalar Tsaro

June 5, 2026

TCN Ta Sanar da Katse Wutar Lantarki a Sassan Delta Saboda Ayyukan Gyaran Tashar Wuta

June 5, 2026
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.