Tsagin jam’iyyar NNPP karkashin jagorancin Dr. Boniface Aniebonam ya zargi Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da hana ta kammala tantance ‘yan takara da gudanar da zabukan fidda gwani gabanin babban zaben shekarar 2027.
Jam’iyyar ta kuma yi barazanar fito da magoya bayanta zanga-zanga a Abuja, tana mai zargin INEC da ci gaba da yin watsi da umarnin kotu kan rikicin shugabancin jam’iyyar.
Tun da farko NNPP ta dakatar da wata zanga-zanga da ta shirya yi wa INEC saboda jinkirin saka sahihin tsarin shugabancinta a shafin hukumar, bayan rokon masu ruwa da tsaki da suka nuna fargabar kutsen bata-gari.
Sai dai cikin wata sanarwa da sakataren jam’iyyar na kasa, Ogini Olaposi, ya fitar a ranar Alhamis, ya ce rashin daukar mataki daga INEC na iya hana jam’iyyar shiga zaben 2027.
“Mun bi duk hanyoyin shari’a domin tilasta wa hukumar bin umarnin kotu da kuma dakatar da jinkirin da muke ganin wasu da suka bar NNPP ke haddasawa,” in ji Olaposi.
Ya kuma ambaci wata ganawa da shugabannin jam’iyyar suka yi da shugaban INEC, Prof. Mahmood Yakubu, tare da sauran jami’an hukumar a Abuja ranar 19 ga Mayu, inda ya ce an ba su fata amma har yanzu babu wani mataki.
“A lokacin shugaban INEC ya ce hukumar za ta dawo mana da amsa nan ba da jimawa ba, amma har yanzu ba ta aiwatar da umarnin kotu da ya ba ta awa 72 ta saka kwamitin gudanarwa na kasa karkashin Dr. Agbo Major ba,” ya bayyana.
Olaposi ya ce kin bin umarnin kotu da INEC ke yi abu ne mai hatsari ga dimokuradiyyar Najeriya, yana mai cewa dole ne hukumar ta mutunta doka.
Ya kara da cewa wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta umarci INEC ta amince da kwamitin Agbo Major, ta cire tsarin Kwankwasiyya karkashin Sanata Rabiu Kwankwaso daga NNPP, sannan ta dawo da tambari da launukan jam’iyyar cikin awa 72.
A cewarsa, duk da hukuncin kotun, INEC har yanzu ba ta aiwatar da umarnin ba bayan sama da kwanaki 60.
Jam’iyyar ta kuma zargi hukumar da nuna bangaranci ta hanyar ci gaba da amincewa da tsarin da ake dangantawa da Kwankwaso duk da zargin cewa wasu manyan ‘yan kungiyar sun koma wata jam’iyya daban.
NNPP ta ce tana da hakkin gudanar da zanga-zangar lumana idan INEC ta ci gaba da kin aiwatar da hukuncin kotu, tana mai jaddada cewa ba za ta amince a hana ta shiga zabe a matsayin halastacciyar jam’iyya ba.
