Close Menu
  • Home
  • News
    • National
    • International
  • Asrah 24 TV
  • Education
  • Health
  • Podcast
  • Politics
  • Sports
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
Facebook X (Twitter) YouTube WhatsApp Telegram
Facebook X (Twitter) WhatsApp Telegram
ASRAH 24 MEDIA
Subscribe
  • Home
  • News
    1. National
    2. International
    3. View All

    CBN Ta Ce Sauye-Sauyen Tattalin Arziki Sun Kafa Tubalin Ci Gaba Da Daidaiton Arzikin Najeriya

    August 6, 2026

    KOTU TA SAMU MACE DA LAIFIN YUNKURIN KASHE ƳAR SHEKARA 9 BAYAN TA YAUDARE TA ZUWA DAJI

    June 26, 2026

    KOTU TA KI SAKIN SOWORE, TA DAGE YANKE HUKUNCI ZUWA 30 GA YUNI

    June 24, 2026

    Sarkin Ilorin Ya Taya Musulmi Murnar Sabuwar Shekarar Hijira, Ya Yi Kiran Hadin Kai

    June 16, 2026

    Hukumar Kula da Mahajjatan Kano Ta Kayyade 25 ga Agusta a Matsayin Ranar Ƙarshe ta Miƙa Fasfo

    August 8, 2026

    📰 Labarin Yanar Gizo (Hausa Version): Kaduna Pilgrims Board Ya Tabbatar An Yi Hadaya Ga Duk Masu Biyan Kuɗi

    June 9, 2026

    Najeriya Ta Fuskanci Limit na Visa zuwa Amurka – 3 Mako Kaɗai!

    July 9, 2025

    Gwamnatin Tarayya Tare da Faransa Za Su Inganta ICT a Jami’o’in Najeriya da Tallafin Naira Biliyan 38

    July 4, 2025

    Hukumar Kula da Mahajjatan Kano Ta Kayyade 25 ga Agusta a Matsayin Ranar Ƙarshe ta Miƙa Fasfo

    August 8, 2026

    Baturen Spain Ya Zo Legas Neman Masu Damfarar Mahaifiyarsa Ta Soyayya

    August 8, 2026

    CBN Ta Ce Sauye-Sauyen Tattalin Arziki Sun Kafa Tubalin Ci Gaba Da Daidaiton Arzikin Najeriya

    August 6, 2026

    Trump Ya Bukaci Kamfanonin Mai Su Rage Farashin Mai Bayan Zargin Samun Ribar Da Ta Yi Yawa

    August 5, 2026
  • Asrah 24 TV
  • Education

    Farfesa Oloyede Ya Ajiye Muƙaminsa a JAMB Bayan Shekaru 10, Ya Koma Koyarwa

    July 31, 2026

    Ɗalibin UNILAG Ya Lashe Gasar Huawei ta ICT ta Duniya a China

    July 31, 2026

    Yajin Aikin ASUU Ya Jefa Daliban Jami’ar AAUA Cikin Rashin Tabbas

    July 27, 2026

    Save the Children Ta Mara Wa Kaduna Baya Don Mayar Da Yara 100,000 Makaranta

    July 24, 2026

    ‘Yar Ministan Abuja Nyesom Wike Ta Samu Digirin Lauya A Birtaniya

    July 22, 2026
  • Health

    ICPC Ta Gurfanar da Likitan El-Rufai Kan Zargin Ƙirƙirar Rahoton Lafiya na Karya Domin Neman Beli

    July 20, 2026

    Masana Sun Yi Gargadin Cewa Gano Cutar Sarcoma Da Wuri Na Iya Taimakawa Wajen Ceto Rayuka

    July 16, 2026

    Kusan Kashi 45% Na Cutar Dementia Ana Iya Hana Ta Ta Hanyar Canza Salon Rayuwa

    July 15, 2026

    Yobe, Qatar Charity Sun Kaddamar da Shirin Kyauta na Duba Ido da Aikin Cataract

    July 15, 2026

    Shahararren Mai Binciken Abinci, Opeyemi Famakin, Ya Ba Da Labarin Yadda Aikin 9-zuwa-5 Ya Gina Rayuwarsa

    July 13, 2026
  • Podcast
  • Politics

    APC Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Ya Nemi Kudancin Kaduna Su Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu Da Uba Sani

    August 8, 2026

    APGA Candidate Ya Janye Waɗa, Ya Goyi Bayan Oyebamiji Na APC

    August 8, 2026

    Uzodimma Ya Mayar Wa Davido Martani Kan Zaɓen Gwamnan Osun

    August 6, 2026

    Zaɓen 15 Ga Agusta Zai Isar Da Saƙo Ga APC – Gwamna Adeleke

    August 6, 2026

    Gwamnatin Tarayya Za Ta Gina Hasumiyoyin Sadarwa 3,700 Domin Haɗa Fiye Da Mutane Miliyan 20 Da Intanet

    August 5, 2026
  • Sports

    Kungiyoyin Premier League Na Gaggawar Kammala Sayayya Kafin Rufe Kasuwar ’Yan Wasa

    August 8, 2026

    Chelsea Ta Lallasa AC Milan 3-0, Ta Lashe Kofin Indonesia Super Cup

    August 8, 2026

    Kasashe 13 Sun Janye Goyon Bayan Infantino Gabanin Zaben Shugabancin FIFA na 2027

    August 8, 2026

    NANS Ta Bukaci ‘Yan Arewa Su Guji Siyasantar Da Gyaran Tsarin Fitar Da Fasfo

    August 6, 2026

    Usyk Ya Bayyana Dangantakarsa Da Anthony Joshua, Ya Goyi Bayan Nasararsa Kan Tyson Fury

    August 2, 2026
  • More
    • Agriculture
    • Business
    • Climate Changes
    • Culture
    • Environment
    • Entertainment
    • Opinion
    • Religious
    • Security
    • Videos
ASRAH 24 MEDIA
Home » NNPP ta zargi INEC da hana ta gudanar da zaben fidda gwani
Politics

NNPP ta zargi INEC da hana ta gudanar da zaben fidda gwani

Asrah24 MediaBy Asrah24 MediaMay 21, 20263 Mins Read
Facebook Twitter WhatsApp
NNPP 720x430

Tsagin jam’iyyar NNPP karkashin jagorancin Dr. Boniface Aniebonam ya zargi Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) da hana ta kammala tantance ‘yan takara da gudanar da zabukan fidda gwani gabanin babban zaben shekarar 2027.

Jam’iyyar ta kuma yi barazanar fito da magoya bayanta zanga-zanga a Abuja, tana mai zargin INEC da ci gaba da yin watsi da umarnin kotu kan rikicin shugabancin jam’iyyar.

Tun da farko NNPP ta dakatar da wata zanga-zanga da ta shirya yi wa INEC saboda jinkirin saka sahihin tsarin shugabancinta a shafin hukumar, bayan rokon masu ruwa da tsaki da suka nuna fargabar kutsen bata-gari.

Sai dai cikin wata sanarwa da sakataren jam’iyyar na kasa, Ogini Olaposi, ya fitar a ranar Alhamis, ya ce rashin daukar mataki daga INEC na iya hana jam’iyyar shiga zaben 2027.

“Mun bi duk hanyoyin shari’a domin tilasta wa hukumar bin umarnin kotu da kuma dakatar da jinkirin da muke ganin wasu da suka bar NNPP ke haddasawa,” in ji Olaposi.

Ya kuma ambaci wata ganawa da shugabannin jam’iyyar suka yi da shugaban INEC, Prof. Mahmood Yakubu, tare da sauran jami’an hukumar a Abuja ranar 19 ga Mayu, inda ya ce an ba su fata amma har yanzu babu wani mataki.

“A lokacin shugaban INEC ya ce hukumar za ta dawo mana da amsa nan ba da jimawa ba, amma har yanzu ba ta aiwatar da umarnin kotu da ya ba ta awa 72 ta saka kwamitin gudanarwa na kasa karkashin Dr. Agbo Major ba,” ya bayyana.

Olaposi ya ce kin bin umarnin kotu da INEC ke yi abu ne mai hatsari ga dimokuradiyyar Najeriya, yana mai cewa dole ne hukumar ta mutunta doka.

Ya kara da cewa wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta umarci INEC ta amince da kwamitin Agbo Major, ta cire tsarin Kwankwasiyya karkashin Sanata Rabiu Kwankwaso daga NNPP, sannan ta dawo da tambari da launukan jam’iyyar cikin awa 72.

A cewarsa, duk da hukuncin kotun, INEC har yanzu ba ta aiwatar da umarnin ba bayan sama da kwanaki 60.

Jam’iyyar ta kuma zargi hukumar da nuna bangaranci ta hanyar ci gaba da amincewa da tsarin da ake dangantawa da Kwankwaso duk da zargin cewa wasu manyan ‘yan kungiyar sun koma wata jam’iyya daban.

NNPP ta ce tana da hakkin gudanar da zanga-zangar lumana idan INEC ta ci gaba da kin aiwatar da hukuncin kotu, tana mai jaddada cewa ba za ta amince a hana ta shiga zabe a matsayin halastacciyar jam’iyya ba.

Share. Facebook Twitter Telegram WhatsApp
Previous ArticleDankwambo ya samu sahalewar PDP domin takarar Sanata a 2027
Next Article Eguavoen ya ce Super Eagles za su fuskanci kalubale a neman gurbin AFCON 2027

Related Posts

APC Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Ya Nemi Kudancin Kaduna Su Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu Da Uba Sani

August 8, 2026

APGA Candidate Ya Janye Waɗa, Ya Goyi Bayan Oyebamiji Na APC

August 8, 2026

Uzodimma Ya Mayar Wa Davido Martani Kan Zaɓen Gwamnan Osun

August 6, 2026

Zaɓen 15 Ga Agusta Zai Isar Da Saƙo Ga APC – Gwamna Adeleke

August 6, 2026
Add A Comment
Leave A Reply Cancel Reply

Latest Posts

APC Mataimakin Ɗan Takarar Gwamnan Kaduna Ya Nemi Kudancin Kaduna Su Ci Gaba Da Goyon Bayan Tinubu Da Uba Sani

August 8, 2026

APGA Candidate Ya Janye Waɗa, Ya Goyi Bayan Oyebamiji Na APC

August 8, 2026

Kada Ku Hana Amarenku Abinci” – Gwamnan Kano Ya Buƙaci Mazajen Da Suka Amfana Da Auren Gata

August 8, 2026

Hukumar Kula da Mahajjatan Kano Ta Kayyade 25 ga Agusta a Matsayin Ranar Ƙarshe ta Miƙa Fasfo

August 8, 2026

Kungiyoyin Premier League Na Gaggawar Kammala Sayayya Kafin Rufe Kasuwar ’Yan Wasa

August 8, 2026
Connect with us
  • Facebook
  • Twitter
  • YouTube
  • WhatsApp
  • Instagram
  • TikTok
Top Posts
Advertisement
© 2026 ASRAH 24 MEDIA. Developed by ENGRMKS & CO..
  • Home
  • About Us
  • Contact Us
  • Privacy Policy

Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.