Fadar Shugaban Kasa ta yi watsi da sabon jawabin tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, kan batun rabon mulki tsakanin Arewa da Kudu, tana mai jaddada cewa ya kamata Kudancin Najeriya ya kammala wa’adinsa kafin zaben 2027.
Mai bai wa Shugaban Kasa shawara kan harkokin yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan a wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na X (tsohon Twitter), inda ya soki matsayin Atiku a matsayin na son kai kuma bisa kuskuren fahimtar tsarin karɓa-karɓa na siyasa tsakanin Arewa da Kudu.
Onanuga ya ce Atiku, a lokacin da yake a jam’iyyar PDP a 2023, ya yi watsi da tsarin rabon mukamai na jam’iyyar ta hanyar neman tsayawa takarar shugabanci duk da cewa ɗan Arewa ne ke kan mulki a lokacin, abin da ya janyo rikici cikin jam’iyyar tare da rage mata ƙarfi a zaɓe.
Ya kuma ƙi amincewa da ikirarin Atiku cewa Arewa ta fi Kudu yawan shekarun mulki tun 1999, inda ya ce ƙarancin shekarun mulkin Arewa ya samo asali ne daga rasuwar tsohon Shugaban Kasa Umaru Musa Yar’Adua a lokacin da yake kan mulki.
A cewarsa, tsarin da ya biyo bayan rasuwar Yar’Adua bai rushe tsarin karɓa-karɓar mulki ba, yana mai cewa hakan “kuskure ne na wucin gadi” ba canjin tsarin siyasa ba.
Onanuga ya jaddada cewa bayan kammala wa’adin shekaru takwas na tsohon Shugaba Muhammadu Buhari, ya dace Shugaba Bola Ahmed Tinubu shima ya kammala nasa wa’adi a karkashin tsarin da ake bi.
Ya kuma ce Atiku ya kamata ya “bar tunanin sake tsayawa takara,” yana mai dagewa cewa har yanzu Kudu ce ta cancanci mulki a 2027.
A nasa bangaren, Atiku ya sha bayyana a wata hira cewa ba ya ɗaure da tsarin rabon mukamai, yana mai cewa yadda aka raba mulki tun 1999 na goyon bayan ra’ayinsa.
Sai dai Fadar Shugaban Kasa ta ce wannan ra’ayi na yin watsi da tsarin siyasa da aka amince da shi a ƙasar.
